ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zagayen Maulidin Annabi (SAW) Ya Gudana Cikin Armashi A Bauchi

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Maulidin Annabi

Kamar kowace shekara, a bana ma al’ummar Musulmai masoya Annabin Tsira, Annabi Muhammad sun fito domin yin zagayen gari domin nuna murna da zagayowar ranar haihuwar Annabi Muhammad (SAW) a cikin garin Bauchi.

Zagayen Maulidin na bana ya kayatar ya kuma samu armashi kana an gudanar da shi lafiya ba tare da wani tashin hankali ko kalubale ba.

  • Maulidi: Duk Wata Wayewa Da Ba Koyi Da Manzon Allah Za Ka Ga Wauta A Cikinta – Sheikh Isma’il

Wakilinmu ya labarto cewa tun safiyar ranar Lahadi ne dai al’ummar musulmai, da kungiyoyin addini, gami da mawaka da sassan masoya Annabin suka fito domin yin wannan jerin gwanon da aka saba gudanarwa duk shekara cikin ado, kwalliya, fareti, wakokin yabon Manzo da sauransu.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda aka saba, dandamin filin kwallo na Kobi shine ke zama mikatin Maulidin a duk shekara kuma makarantun Islamiyoyi ne ke fara shiga sawu, inda ake fita bisa layi tare da nizami, haka a bana ma zancen ya gudana, inda masu maulidin suka taso daga Kobi, suka nausa kofar Fadar Sarkin Bauchi, Dakta Rilwanu Sulaiman Adamu inda suke mika masa gaisuwar Maulidin yayin da shi kuma ke saman fadarsa zaune na amsar gaisuwar.

Maulidin Annabi
Baya ga hakan, masu zagayen sun nausa zuwa titin Santaral, suka nufi titin Kofaran da zarcewa Bakin Kura, zuwa Tashan Babiye kana layin ya wuce zuwa titin Wunti da sauran manyan hanyoyin jihar dukka domin nuna farin ciki da wannan ranar ta Maulidi.
A gefe daya, masu maulidin kan raba kyautuka da alawa da fulawowi ga masu kallonsu, a yayin da su masu kallon ke mika kyautuka ga wadanda suke kan sahun Maulidin. Inda zagayen ke kara dankon kauna da fahimtar juna a tskanin bangarori daban-daban.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Da muke zantawa da daya daga cikin malaman addinin musulunci kuma almajirin Sheikh Dahiru Usman Bauchi, Malam Muhammadu Sunusi, ya bayyana cewar suna fitowa zagayen Maulidin ne domin nuna kauna da soyayya ga Annabi Muhammad (S), har ma ya ce zagayen na baya ya kayatar sosai.

“Alhamdullahi zagayen baya sai godiya wa Allah domin an samu sauye-sauye da gyare-gyare da suka kara inganta zagayen na bana.
“Muna fitowa zagayen Maulidin nan ne domin Allah domin Annabi (S), ka ga dai da idonka babu wani abun da ake yi da aka daina, maza da mata, yara da kanana, tsoffi kowa ya fito domin nuna murnarsa da zagayowar wannan ranar kuma cikin tsari.

Maulidin Annabi
“Kuma abun da ake yi dai shine aka saba, wato raya yabon Manzon Allah (SAW), nuna soyayayarsa da tunawa ma jama’a Manzon nan da yaren labaranci, Hausa ga wasu ma da sifa da shiga irin na Yarbawa da Inyamurai wasu Fulani haka aka kayatar da wunin nan gaba daya tun safe har dare Manzon Allah ake anbato a jihar nan domin duniya ta shaidi mun yi wa Allah godiya a kan wannan ni’ima da ya yi mana.”

Malamin ya ce godiya ne suke yi da ni’imar da Allah ya musu, yana mai cewa babu wata ni’ima da ta kai samun Manzon Allah.
“Don haka muka fito domin nuna godiya da wannan ni’ima, da rahama da aka samu sakamakon zuwan Manzon Allah.”

Sunusi wanda ake wa lakabi da fiya-fiya, ya kuma nuna cewa an yi taron lafiya an kammala lafiya don haka ne suke kara godiya ga Allaha kan hakan, “Masu sukar Maulidi ya kamata zagayen da ake yi ya zama musu wa’azi na cewa ya kamata su daina domin hakan ba ya rage komai sai kara armashi wa Maulidi.”
Muhammadu Sunisi ya yi fatan Allah maimaita kana ya nuna gamsuwarsa da yadda aka yi tsari masu kyau wajen gudanar da maulidin cikin kwanciyar hankali da annashuwa.

Maulidin Annabi
Shi ma da yake zantawa da ‘yan jarida kan wannan zagayen, wakilin ‘yan uwa musulmai Almajiran Sheikh Zakzaky a jihar Bauchi, Malam Ahmad Yusuf Yashi, ya yi amfani da wannan damar wajen kira ga jama’a da su dauki maulidi a matsayin babban alamin hadin kai da inganta zaman lafiya a tsakanin jama’a.

“Kamar kowace shekara a bana ma ranar 12 ga watan Rabi’u Auwal mun fito ne domin nuna farin ciki da zagayowar ranar haihuwar Manzon Rahma, Muhammadu Dan Abdullahi (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi), kuma alhamudullahi ba mu kadai ma al’umma gata nan gabaki daya an fito domin yin musharaka wajen nuna wannan farin cikin.

“Sakona a irin wannan rana shine cewa mu yi amfani da wannan dama wajen dinke baraka a tsakanin al’ummar musulmai, duk da banbance-banbancen da ke akwai, tun da Manzon Allah ya hadamu, Kaaaba ta hadamu mu yi amfani da wannan damar mu zauna mu dinke mu zama abu guda domin cigaban al’ummar musulmai da jama’a gabaki daya,” Inji Yashi.

Maulidin Annabi
A sakonsa na fatan alkairi ga masu zagayen Maulidin, Sarkin Bauchi, Dakta Rilwanu Sulaiman Adamu ya nuna farin cikinsa kan yadda zagayen na bana ya gudana cikin kwanciyar hankali da armashi, sai ya yi kira kan kara hada kai da fahimtar juna a tsakanin al’umma domin rayuwa take ingantuwa a jihar.

Ya kuma yi fatan Allah maimaita tare da taya al’umma murnar zagayowar wannan maulidin na 2022.
A sakonsa na ranar Maulidi da gwamnan Bala Muhammad ya fitar, ya taya al’ummar musulmai murnar zagayowar ranar Maulidi tare da rokonsu da su kasance masu koyi da dabi’un Manzo.

A sakon da ya fitar ta hannun kakakinsa, Muktar Gidado, gwamnan ya ce dukkanin rayuwar Manzon Allah abin koyi ne ga al’umma, kuma a cewarsa, Annabi ya koyar da zaman lafiya, kwanciyar hankali, kyauta, Dabi’u na kwarai, don haka ne ya nemi al’umma da su yi koyi domin kyautata zaman lafiya a jihar da kasa baki daya.

Gwamnan ya yi fatan cewa jama’a za su yi addu’ar zaman lafiya da kwanciyar hankali ga kasa a yayin da suke gudanar da shagulan bikin Maulidi na bana.

Daga bisani ya yi fatan cewa za a gudanar da taron Maulidin a ciki da wajen jihar lafiya kamar yadda aka fara cikin kwanciyar hankali. Sanann, ya nemi jama’a da su kara yi wa gwamantinsa addu’a domin ta cimma nasarorin da ta sanya a gaba.

Shi kuma Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya bukaci jama’a da su yi addu’ar samun shugabanni na kwarai da gudanar da zaben 2023 cikin kwanciyar hankali.

Da yake jawabi a wajen taron Maulidin da ya saba shiryawa na bana, Dahiru ya ce suna gudanar da Maulidin ne domin raya ranar da aka haifi Manzon Allah (SAW), ya kuma jawo hankalin al’umma da su cigaba da koyi da halayen Manzon Allah a kowani lokaci.

Maulidin Annabi
Shi kuma a jawabinsa a wajen taron Maulidin Manzon Allah da Sheikh Dahiru Bauchi ya shirya, gwamnan Jihar Bala Muhammad ya ce juriya, sadaukarwa, zaman lafiya, taimako da neman ilimi na cikin ababen da Manzon Allah ya koyar da sahabban sa masu daraja, don haka ne ya nemi al’umma da su yi koyi.

Gwamna Bala Muhammad ya bukaci Malamai da su daina sukar shugabanni a gaban dalibansu ba tare da kwararan hujjoji ba domin kyautata rayuwa a kowani lokaci.

Maulidin Annabi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Na Amince Zan Goyi Bayan Takarar Atiku Abubakar —Wike

Na Amince Zan Goyi Bayan Takarar Atiku Abubakar —Wike

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.