• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

by Rabilu Sanusi Bena
2 months ago
in Nishadi
0
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abba Sadau, ‘ya’yan fitacciyar jaruma Rahama Sadau, ya bayyana alhini kan rasuwar mahaifinsu, Alhaji Ibrahim Sadau, wanda ya kwanta dama a ranar 22 ga watan Yunin da ya gabata, mahaifin nasu dai; ya rasu ne da sanyin safiyar ranar Talata, kwana daya bayan dawowarsa daga aikin Hajji, ya rasu a asibitin sojoji na 44, da ke Jihar Kaduna da misalin karfe 4:00 na asuba, sanadiyar ciwon Siga.

Mujallar Fim ta ruwaito cewa, an yi jana’idarsa da misalin karfe 10:00 na safiyar ranar da ya rasu, a harabar wata makarantar Islamiyya da ke kusa da gidansa, a kan titin Lome da ke Unguwar Rimi.

  • INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12
  • 2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

Dattijon mai kimanin shekara 58, ya rasu ya bar mata biyu da ‘ya’ya tara, daga cikinsu akwai jaruma a masana’antar Kannywood, Rahama Sadau; wacce ita ce ‘yarsa ta biyu.

Daya daga cikin ‘ya’yan mamacin, Furodusa Haruna Sadau lbrahim, wanda aka fi sani da Abba Sadau; ya bayyana irin halin kidimewa da ya shiga, sakamakon wancan rashi na mahaifin nasu. Abba, wanda furodusa ne a masana’antar Kannywood, ya ce, “Inna lillahi wa inna ilaihir raji’un, wannan rashi ba mu taba yin irinsa ba a danginmu baki-daya, wannan shi ne karo na farko da muka yi irin wannan rashi babba.

“Wannan rashi ya yi matukar taba mu, ya taba kowa da kowa. Domin kuuwa, ni har yanzu ban gama yarda cewa ya mutu ba; bayan dawowarsa daga Saudiyya, ya ce; ba shi da lafiya, daga nan sai ya kira ni a waya ya ce da ni na turo masa likita, sai na ce da shi; kamata ya yi ya je asibiti a duba shi sosai, ana kai shi asibitin, sai labari ya canza; jikin nasa ya yi tsanani sosai”, in ji Abba.

Labarai Masu Nasaba

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

Sadau, ya ci gaba da bayyana yadda zai ci gaba rika tunawa da mahaifin nasu, inda ya ce; “Akwai abubuwa da dama da zan rika tuna mahaifina da su, amma abin da zan fi tunawa da shi, wanda kuma zan yi koyi da su shi ne kula da ibada, domin ba za a taba zuwa masallaci ka gan shi a sahu na biyu ba, koda-yaushe a sahun farko za ka gan shi. In dai ibada ce, a gaba za ka gan shi; an shaide shi da haka”, in ji shi.

“Ina godiya ga yan Kannywood da sauran al’ummar da suka halarci jana’iza, wallahi har kwalla na yi saboda irin dandazon jama’a da na gani, Allah ya saka wa kowa da alhairi, sannan kuma ya ba mu hakurin rashin wannan mahaifi namu, muna fatan yadda ya samu kyakkyawar shaida a wajen mutane, ya sa ya samu wannan a can”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Sadau
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

Next Post

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Related

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Nishadi

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

5 days ago
Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba
Nishadi

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

2 weeks ago
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah
Nishadi

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

3 weeks ago
Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

4 weeks ago
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu
Nishadi

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

1 month ago
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya
Nishadi

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

1 month ago
Next Post
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

LABARAI MASU NASABA

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

September 12, 2025
Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

September 12, 2025
Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

September 12, 2025
Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

September 12, 2025
Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

September 12, 2025
Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

September 12, 2025
Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

September 12, 2025
Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

September 12, 2025
Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

September 12, 2025
Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.