• English
  • Business News
Tuesday, October 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Tabbatar Da Dawo Da Asalin Tsarin Abuja ‘Zan Tsaya Kan Kafafuna’, – Wike

byKhalid Idris Doya
2 years ago
Wike

Sabon rantsatstsen ministan babban birnin tarayya Abuja (FCT), Nyesom Wike, ya shiga ofis domin kama aiki a ranar Litinin, inda ya yi gargadin cewa zai tsaya tsayin daka kan kafafunsa wajen gudanar da aikinsa domin kwato da dawo da asalin tsarin taswirar birnin tarayya Abuja.

 

A cewar Wike, dukkanin wani ko wasu da suka yi gini a muhallin da bai dace su yi gini ba, tun da wuri su kwan da sanin cewa za a fa a rashe wannan ginin babu makawa.

  • Tinubu Ya Bukaci Sabbin Ministoci Kan Su Yi Aiki Tukuru Don Biyan Bukatun ‘Yan Nijeriya

Ya ce, baya ga kokarin dawo da asalin zubin tsarin birnin tarayya da zai maida hankali a kai, zan yi aikin hadin guiwa da hukumomin tsaro domin tabbatar da tsaro mai inganci a cikin birnin tarayya.

 

LABARAI MASU NASABA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

Ya tabbatar wa mazauna FCT cewa zai yi duk mai yiyu wajen magance matsalolin tsaro da kuma tabbatar da doka da oda a tsarin bunkasa filaye da gine-gine.

 

“A shirye muke mu samar da kayan aiki ga dukkanin hukumomin tsaro domin su gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

 

“Idan na samar da dukkanin abubuwan bukata ga hukumomin tsaro, ba zan amshi wani uzuri ba.

 

“Meye muke so, kawai sakamako, kuma dole hakan ya faru. Idan ba mu kare nan wajen ba, to muna cikin matsala kuwa.

 

“Ka ga mutane su saci wannan abun su saci wancan. Wake da alhaki? Ina jami’an tsaro suke? Dole a yi wani abu domin dakile hakan.

 

“Batun tsaro manufarmu ne baki daya. Shugaban kasa ya fada min, ko ma yaya ne dai, dole ne mu tabbatar da samar da tsaro ga Abuja, dole ne mu tabbatar ta samu kwanciyar hankali.

 

“Ba za mu lamunci dabi’ar ganin ko’ina ya zama kasuwanni ba. A’a, ba za mu amince da hakan ba. Eh, na sani abubuwan ba za su zo da sauki ba, amma ba shi ne ke nuni da cewa sai ka haifar da rikici ga wasu mutane ba,” Wike ya shaida.

 

A wani mataki na gargadi, ministan ya gargadi dukkanin masu mamayar filaye ta hanyoyin da basu da cewa da cewa, “Idan kun san kun shimfida gini a inda bai kamata ku shinfida ba, ka sani gidanka fa dole ya sha kasa.”

 

Kazalika, ya gargadi masu bada gidajen haya ba bisa ka’ida ba, da su shiga taitayinsu. Kana ya nemi mutane da su ke mallakar shaidar mallaka (CofOs) na filayensu.

 

“Zan tsaya a kan yatsuna, na babban ma kuwa, kuma zan take naku kafafu da yatsun idan kuna yin ba daidai ba,” Wike ya tabbatar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci
Labarai

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Next Post
Gwamna Uba Sani Ya Sake Nadin Sabbin Mukamai A Jihar Kaduna 

Gwamna Uba Sani Ya Rage Kudin Manyan Makarantun Jihar Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Na Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Korea Ta Arewa

Firaministan Sin Zai Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Na Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Korea Ta Arewa

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version