• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Tabbatar Da Dawo Da Asalin Tsarin Abuja ‘Zan Tsaya Kan Kafafuna’, – Wike

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Zan Tabbatar Da Dawo Da Asalin Tsarin Abuja ‘Zan Tsaya Kan Kafafuna’, – Wike
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sabon rantsatstsen ministan babban birnin tarayya Abuja (FCT), Nyesom Wike, ya shiga ofis domin kama aiki a ranar Litinin, inda ya yi gargadin cewa zai tsaya tsayin daka kan kafafunsa wajen gudanar da aikinsa domin kwato da dawo da asalin tsarin taswirar birnin tarayya Abuja.

 

A cewar Wike, dukkanin wani ko wasu da suka yi gini a muhallin da bai dace su yi gini ba, tun da wuri su kwan da sanin cewa za a fa a rashe wannan ginin babu makawa.

  • Tinubu Ya Bukaci Sabbin Ministoci Kan Su Yi Aiki Tukuru Don Biyan Bukatun ‘Yan Nijeriya

Ya ce, baya ga kokarin dawo da asalin zubin tsarin birnin tarayya da zai maida hankali a kai, zan yi aikin hadin guiwa da hukumomin tsaro domin tabbatar da tsaro mai inganci a cikin birnin tarayya.

 

Labarai Masu Nasaba

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Ya tabbatar wa mazauna FCT cewa zai yi duk mai yiyu wajen magance matsalolin tsaro da kuma tabbatar da doka da oda a tsarin bunkasa filaye da gine-gine.

 

“A shirye muke mu samar da kayan aiki ga dukkanin hukumomin tsaro domin su gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

 

“Idan na samar da dukkanin abubuwan bukata ga hukumomin tsaro, ba zan amshi wani uzuri ba.

 

“Meye muke so, kawai sakamako, kuma dole hakan ya faru. Idan ba mu kare nan wajen ba, to muna cikin matsala kuwa.

 

“Ka ga mutane su saci wannan abun su saci wancan. Wake da alhaki? Ina jami’an tsaro suke? Dole a yi wani abu domin dakile hakan.

 

“Batun tsaro manufarmu ne baki daya. Shugaban kasa ya fada min, ko ma yaya ne dai, dole ne mu tabbatar da samar da tsaro ga Abuja, dole ne mu tabbatar ta samu kwanciyar hankali.

 

“Ba za mu lamunci dabi’ar ganin ko’ina ya zama kasuwanni ba. A’a, ba za mu amince da hakan ba. Eh, na sani abubuwan ba za su zo da sauki ba, amma ba shi ne ke nuni da cewa sai ka haifar da rikici ga wasu mutane ba,” Wike ya shaida.

 

A wani mataki na gargadi, ministan ya gargadi dukkanin masu mamayar filaye ta hanyoyin da basu da cewa da cewa, “Idan kun san kun shimfida gini a inda bai kamata ku shinfida ba, ka sani gidanka fa dole ya sha kasa.”

 

Kazalika, ya gargadi masu bada gidajen haya ba bisa ka’ida ba, da su shiga taitayinsu. Kana ya nemi mutane da su ke mallakar shaidar mallaka (CofOs) na filayensu.

 

“Zan tsaya a kan yatsuna, na babban ma kuwa, kuma zan take naku kafafu da yatsun idan kuna yin ba daidai ba,” Wike ya tabbatar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abuja
ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Da Kafofin Watsa Labaran Afirka Sun Kulla Sabuwar Yarjejeniyar Hadin Gwiwa

Next Post

Gwamna Uba Sani Ya Rage Kudin Manyan Makarantun Jihar Kaduna

Related

Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC
Labarai

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

2 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

4 hours ago
Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

5 hours ago
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya
Labarai

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

6 hours ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

8 hours ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

8 hours ago
Next Post
Gwamna Uba Sani Ya Sake Nadin Sabbin Mukamai A Jihar Kaduna 

Gwamna Uba Sani Ya Rage Kudin Manyan Makarantun Jihar Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.