• English
  • Business News
Friday, August 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Tabbatar Da Dawo Da Asalin Tsarin Abuja ‘Zan Tsaya Kan Kafafuna’, – Wike

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Zan Tabbatar Da Dawo Da Asalin Tsarin Abuja ‘Zan Tsaya Kan Kafafuna’, – Wike
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sabon rantsatstsen ministan babban birnin tarayya Abuja (FCT), Nyesom Wike, ya shiga ofis domin kama aiki a ranar Litinin, inda ya yi gargadin cewa zai tsaya tsayin daka kan kafafunsa wajen gudanar da aikinsa domin kwato da dawo da asalin tsarin taswirar birnin tarayya Abuja.

 

A cewar Wike, dukkanin wani ko wasu da suka yi gini a muhallin da bai dace su yi gini ba, tun da wuri su kwan da sanin cewa za a fa a rashe wannan ginin babu makawa.

  • Tinubu Ya Bukaci Sabbin Ministoci Kan Su Yi Aiki Tukuru Don Biyan Bukatun ‘Yan Nijeriya

Ya ce, baya ga kokarin dawo da asalin zubin tsarin birnin tarayya da zai maida hankali a kai, zan yi aikin hadin guiwa da hukumomin tsaro domin tabbatar da tsaro mai inganci a cikin birnin tarayya.

 

Labarai Masu Nasaba

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Ya tabbatar wa mazauna FCT cewa zai yi duk mai yiyu wajen magance matsalolin tsaro da kuma tabbatar da doka da oda a tsarin bunkasa filaye da gine-gine.

 

“A shirye muke mu samar da kayan aiki ga dukkanin hukumomin tsaro domin su gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

 

“Idan na samar da dukkanin abubuwan bukata ga hukumomin tsaro, ba zan amshi wani uzuri ba.

 

“Meye muke so, kawai sakamako, kuma dole hakan ya faru. Idan ba mu kare nan wajen ba, to muna cikin matsala kuwa.

 

“Ka ga mutane su saci wannan abun su saci wancan. Wake da alhaki? Ina jami’an tsaro suke? Dole a yi wani abu domin dakile hakan.

 

“Batun tsaro manufarmu ne baki daya. Shugaban kasa ya fada min, ko ma yaya ne dai, dole ne mu tabbatar da samar da tsaro ga Abuja, dole ne mu tabbatar ta samu kwanciyar hankali.

 

“Ba za mu lamunci dabi’ar ganin ko’ina ya zama kasuwanni ba. A’a, ba za mu amince da hakan ba. Eh, na sani abubuwan ba za su zo da sauki ba, amma ba shi ne ke nuni da cewa sai ka haifar da rikici ga wasu mutane ba,” Wike ya shaida.

 

A wani mataki na gargadi, ministan ya gargadi dukkanin masu mamayar filaye ta hanyoyin da basu da cewa da cewa, “Idan kun san kun shimfida gini a inda bai kamata ku shinfida ba, ka sani gidanka fa dole ya sha kasa.”

 

Kazalika, ya gargadi masu bada gidajen haya ba bisa ka’ida ba, da su shiga taitayinsu. Kana ya nemi mutane da su ke mallakar shaidar mallaka (CofOs) na filayensu.

 

“Zan tsaya a kan yatsuna, na babban ma kuwa, kuma zan take naku kafafu da yatsun idan kuna yin ba daidai ba,” Wike ya tabbatar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abuja
ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Da Kafofin Watsa Labaran Afirka Sun Kulla Sabuwar Yarjejeniyar Hadin Gwiwa

Next Post

Gwamna Uba Sani Ya Rage Kudin Manyan Makarantun Jihar Kaduna

Related

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

1 hour ago
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

2 hours ago
Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista
Labarai

Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista

7 hours ago
GORON JUMA’A 01-07-2025
Labarai

GORON JUMA’A 01-07-2025

9 hours ago
An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano
Manyan Labarai

An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

10 hours ago
Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin
Manyan Labarai

Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin

12 hours ago
Next Post
Gwamna Uba Sani Ya Sake Nadin Sabbin Mukamai A Jihar Kaduna 

Gwamna Uba Sani Ya Rage Kudin Manyan Makarantun Jihar Kaduna

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

August 1, 2025
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

August 1, 2025
Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6

Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6

August 1, 2025
Sin Ta Samarwa Sassan Kasa Da Kasa Damar Shigowa Ba Tare Da Bukatar Biza Ba

Sin Ta Samarwa Sassan Kasa Da Kasa Damar Shigowa Ba Tare Da Bukatar Biza Ba

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.