ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Tabbatar Da Dawo Da Asalin Tsarin Abuja ‘Zan Tsaya Kan Kafafuna’, – Wike

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Wike

Sabon rantsatstsen ministan babban birnin tarayya Abuja (FCT), Nyesom Wike, ya shiga ofis domin kama aiki a ranar Litinin, inda ya yi gargadin cewa zai tsaya tsayin daka kan kafafunsa wajen gudanar da aikinsa domin kwato da dawo da asalin tsarin taswirar birnin tarayya Abuja.

 

A cewar Wike, dukkanin wani ko wasu da suka yi gini a muhallin da bai dace su yi gini ba, tun da wuri su kwan da sanin cewa za a fa a rashe wannan ginin babu makawa.

ADVERTISEMENT
  • Tinubu Ya Bukaci Sabbin Ministoci Kan Su Yi Aiki Tukuru Don Biyan Bukatun ‘Yan Nijeriya

Ya ce, baya ga kokarin dawo da asalin zubin tsarin birnin tarayya da zai maida hankali a kai, zan yi aikin hadin guiwa da hukumomin tsaro domin tabbatar da tsaro mai inganci a cikin birnin tarayya.

 

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Ya tabbatar wa mazauna FCT cewa zai yi duk mai yiyu wajen magance matsalolin tsaro da kuma tabbatar da doka da oda a tsarin bunkasa filaye da gine-gine.

 

“A shirye muke mu samar da kayan aiki ga dukkanin hukumomin tsaro domin su gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

 

“Idan na samar da dukkanin abubuwan bukata ga hukumomin tsaro, ba zan amshi wani uzuri ba.

 

“Meye muke so, kawai sakamako, kuma dole hakan ya faru. Idan ba mu kare nan wajen ba, to muna cikin matsala kuwa.

 

“Ka ga mutane su saci wannan abun su saci wancan. Wake da alhaki? Ina jami’an tsaro suke? Dole a yi wani abu domin dakile hakan.

 

“Batun tsaro manufarmu ne baki daya. Shugaban kasa ya fada min, ko ma yaya ne dai, dole ne mu tabbatar da samar da tsaro ga Abuja, dole ne mu tabbatar ta samu kwanciyar hankali.

 

“Ba za mu lamunci dabi’ar ganin ko’ina ya zama kasuwanni ba. A’a, ba za mu amince da hakan ba. Eh, na sani abubuwan ba za su zo da sauki ba, amma ba shi ne ke nuni da cewa sai ka haifar da rikici ga wasu mutane ba,” Wike ya shaida.

 

A wani mataki na gargadi, ministan ya gargadi dukkanin masu mamayar filaye ta hanyoyin da basu da cewa da cewa, “Idan kun san kun shimfida gini a inda bai kamata ku shinfida ba, ka sani gidanka fa dole ya sha kasa.”

 

Kazalika, ya gargadi masu bada gidajen haya ba bisa ka’ida ba, da su shiga taitayinsu. Kana ya nemi mutane da su ke mallakar shaidar mallaka (CofOs) na filayensu.

 

“Zan tsaya a kan yatsuna, na babban ma kuwa, kuma zan take naku kafafu da yatsun idan kuna yin ba daidai ba,” Wike ya tabbatar.

Wike
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Next Post
Gwamna Uba Sani Ya Sake Nadin Sabbin Mukamai A Jihar Kaduna 

Gwamna Uba Sani Ya Rage Kudin Manyan Makarantun Jihar Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.