• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

by Leadership Hausa
3 months ago
in Manyan Labarai
0
Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Zanga-zangar da ‘yan gudun hijira biyo bayan hare-haren da ya tarwatsasu daga matsugnanunsu da ke a yankin Yelwata, na jihar Biniwe, hakan ya nuna a zahiri, na irin yanayin yin watsi da ‘yan gudun hijira a kasar.

Sun yi zanga-zngar ce, a wasu manyan titnun kamar na George Akume da ke a Makurdi, babban birinin jihar, a ranar 19 na watan Yunin, 2025.

  • Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
  • Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram

Sun datse hanyoyin, domin su nuna bacin ransu, na barinsu na yin watsi da su a sansaninsu da barinsu a cikin yanwa da kuma karkatar da kayan da aka turo masu na dauki.

Abin takaici ne, duba da yadda ake samun sansanin ‘yan gudun hijira a kasar makare da masu gudun hijira, ba tare da an tanadar masu da kayan more rayuwa ba, wanda rashin hakan, ke janyo mutuwar wasunsu.

Tabbas, irin wannan halin da suke ciki, abu ne, da ke bukatar a dauki matakan gaggawa, domin magance wadannan matsalolin.

Labarai Masu Nasaba

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Kazalika, gazawar Hukumar Bayar Da Agajin Gaggawa ta Kasa NEMA da kuma sauran hukumomin na jihohi na sauke nauyinsu, hakan ya nuna a zahiri, na irin kalubalen da ake fuskanta, na rashin sauke nauyinsu, na bayar da agajin na gaggawa.

Misalii, an ruwaito cewa, a sansanin na ‘yan gudun hijira na Yelwata, musamman yadda suke kwana a kan tandarmin kasa, tare da kokawa da cizon Sauro, ‘ya’yansu ke ci gaba da zama a cikin yunwa, wanda hakan, ya kara harzuka su, fita yin zanga-zangar.

Bisa wasu akaluma da aka samu daga Biniwe, sun nuna cewa, a sansanin na Yelwata, an samu haihuwa 15 da kuma mata da suka samu juna biyu, su 122, wadanda kuma suke ci gaba da rashin samun kulawar kiwon lafiyarsu, hakan kuma ya jefa, rayuwar jariransu, a cikin hadari.

Bugu da kari, a sansanin ‘yan gudun hijira na jihar Nasarawa, an samu kwararowar sama da ‘yan gudun hijira guda 4,000 daga sansanin ‘yan gudun hijira na Biniwe.

Wannan ya zama wani babban nauyin wajen ciyar da su da kuma rashin samar masu da wajen wadatattun wajen kwana da rashin tsafta.

Kusan a daukacin sansanonin ‘yan gudun hijira, kamar na jihohin Borno da Adamawa, dubban ‘yan gudun hijirar da yaki da ‘yan ta’addar Boko Haram ya tarwatsa su daga matsugunan su, suna ci gaba da fuskantar karancin ruwan sha, magunguna, inda kuma ake samun barkewar Kwalara, wanda hakan, ke janyo rasa rayukan wadanda lamarin ya rutsa da su.

Wadannan misalan kadai, sun nuna irin rashin gazawar kula da yanayin da bil’Adama ke ciki.

Hukumar NEMA, wadda aka dora mata nauyin bayar da dauki kan aukuwar annoba, ta gaza sauke wannan nayin nata.

Sai dai, har yanzu zamu ci gaba da yin magana domin NEMA ta sauke nauyin da aka dora mata, musamman na bayar da agajin na gaggawa ga wadanda wani iftila’i, ya fada masu.

Kazalika, kayan agajin da Hukumar ta tura zuwa sansani na Yelwata, bayan kai hare-haren a yankin, idan aka yi dubi da lokacin da aka kai kayan da rashin kai wadatattunsu, wannan babban abin tambaya ne da har yanzu, ke bukatar amsa, musamman, kan yadda aka zargin wasu jami’an na NEMA, na karkatar da kayan na agajin.

Bugu da kari, hakan ya nuna irin yadda a 2024, NEMA ta fuskanci suka da zargi, na boye kayan da ya kamata a rabawa ‘yan gudun hijira a dakunanta na adana kayan agaji, wanda hakan ya jefa rayuwar ‘yan gudun hijira, musamman wadanda ke a Arewa Masu Gabas, a cikin kuncin rayuwa.

A dai jihar ta Biniwe, Hukumar Bayar Da Agajin Gaggawa ta jihar SEMA, ta fuskanci suka kan yin watsi da ‘yan gudun hijira na Yelwata, musamman duba da yadda aka barsu, a cikin kangin yunwa, cizon Sauro, wanda kuma aka yi zargin, wasu jami’an na SEMA, sun karkatar da kayan agajin, da ya kamata a raba masu.

Hakan ma batun ma yake a jihar Adamawa, inda aka zargi Hukumar SEMA ta jihar, kan kin rabar masu da kayan dauki kan lokaci, wanda hakan ya haifar da zanga-zanga a watan Mayun 2025.

Sai dai, wadanan Hukumomin suna bugewa da dora laifin kan rashin ba su kudaden da ya kamata Gwamnatin Tarayya ta tura masu.

Hakazalika, rashin taka rawar da ya kamata ‘yan majalisu da matakan gwamnati ya kamata su yi, na rabar da kayan dauki ga alumma, hakan ya kara kawo rudani, kan batun na bayar da daukin.

Shirye-shiryen rabar da kayan tallafin rage radadin kuncin rayuwa, hakan ya sanya an fifita mazauna birane da ‘yan lelen ‘yan siyasa, inda su kuma ‘yan gudun hijira, aka mayar da su, saniyar ware.

A jihar ta Biniwe duk da kudaden da gwamnatin jihar kebewa da kananan hukumomin jihar da kuma wanda take kebewa sarakunan gargajiya, amma abin bakin cikin shi ne, ba kebe kudaden, da ya kamata a tallafawa ‘yan gudun hijira na jihar, inda gwamnatin ke fakewa, da cewa, tana fuskantar karancin kudade.

Karkatar da kayan agajin da ya kamata a kai wa ‘yan gudun hijirar na Yelwata, hakan ya nuna cewa, ba a dauki rayuwarsu, da wata mahimmanci ba.

Bisa ra’ayin wannan Jaridar, ya zama wajibi zababbun ‘yan majalisar kasar, su mayar da hankali wajen fifita kula da rayuwar ‘yan gudun hijira, musamman ta hanyar kebe masu wani gwa-gwaban kaso a cikin kasafin kudi na kasar da kuma kirkiro da dokokin da za su tabbatar da an yi adalci, wajen rabar masu da kayan tallafi da kuma daukar kwakwaran hukunci, ga duk wanda ya karkatar da kayan tallafin da aka yi niyyar kai masu.

Bugu da kari, ya zama wajbi matakan gwamnati uku na kasar da su kebe kudade da za a rinka taimaka wa ‘yan gudun hijira kai tsaye da ke a sansanonin su da samar masu da abinci, da kayan kula da lafiyarsu da wajen kwana da kuma sanya ido kan kayan domin a dakile yin cuwa-cuwa da kayan.

Ya zama wajbi kananan hukumomi da masarautu da gwamnatin jihohi ke tallafa masu da kudaden gudanar da ayyukansu, su yi hadaka da jagororin alummomi domin su gano tare da ganin ana tallafa wa ‘yan gudun hijirar, yadda ya dace.

Hakazalika, ya zama wajibi, a yiwa hukumomin NEMA da SEMA garanbawul, musamman domin a dawo da ainahin kimarsu, yadda ya kamata.

Zanga-zangar ta ‘yan gudun hijirar na Yelwata, wata ‘yar manuniya ce, da ke nuni da cewa, ya zama wajbi, a dauki matakan da suka wajaba, na irin halin da suke ciki.

Duba da cewa, a Nijeriya akwai ‘yan gudun hijira da yawansu ya kai sama da miliyan uku, hakan ya nuna cewa, ba wai kawai alkarin baki ya suka cancanta ba, amma kula da rayuwarsu, yadda ta kama, shi ne mafita.

Kazalika, duba da cewa, ana cikin yanayi na damina a kasar, akwai kuma wani karin barazanar da ke tafe, mai yuwa za a iya samun ambaliyar rayuwan sama wanda hakan zai janyo tarwatsa alumomi daga matsugunasu, inda hakan ya nuna cewa, tun yanzu, ya zama waji, a dauki matakan gaggawa.

Ya kamata ‘yan majalisa da shugabannin kananan hukomin da sarakunan gargajiya, su nuna cewa, da gaske suke wajen jin kan rayuwar ‘yan gudun hijira, sama da na su kudurorin na kashin kansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: YelewataZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

Next Post

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Sa Mata Da Jarirai Mutuwa Yayin Haihuwa

Related

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

9 hours ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

10 hours ago
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban
Manyan Labarai

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

20 hours ago
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi
Manyan Labarai

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

21 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

1 day ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

1 day ago
Next Post
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Sa Mata Da Jarirai Mutuwa Yayin Haihuwa

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Sa Mata Da Jarirai Mutuwa Yayin Haihuwa

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Zanga-zangar

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.