• English
  • Business News
Wednesday, July 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Almundahanar Biliyan ₦2.8b: EFCC Ta Gurfanar Da Hadi Sirika

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Zargin Almundahanar Biliyan ₦2.8b: EFCC Ta Gurfanar Da Hadi Sirika
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Alleged N2.8bn Fraud: EFCC Opens Case Against Sirika, Others

Zargin Almundahanar Biliyan ₦2.8b: EFCC Ta Gurfanar Da Hadi Sirika Gaban Kotu

Hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa, EFCC, ta fara tuhumar tsohon ministan sufurin jiragen sama, Hadi Sirika da wasu mutane uku, bisa zargin almundahanar Naira biliyan 2.6.

Sirika, tare da ɗiyar sa Fatima, Jalal Sule Hamma, da kuma Al-Duraq Investment Limited, suna fuskantar tuhume-tuhume guda shida da suka haɗa da zamba a ofis da kuma badaƙalar kwangila a babbar kotun birnin tarayya (FCT) dake Maitama.

  • Badakalar Fiye Da Biliyan 8: EFCC Ta Cafke Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Hadi Sirika 
  • Almundahana: Kotu Ta Bayar Da Belin Hadi Sirika Da ‘Yarsa

Shaidu na farko na EFCC, Azubuike Okorie, tsohon ma’aikacin ma’aikatar sufurin jiragen sama, ya shaida rawar da ya taka a matsayinsa na Daraktan saye da sayarwa da kuma mataimaki na musamman ga Ministan, inda ya bayyana ayyukan sa na sa ido da tantance ayyuka, duk da cewa ba shi da hannu kai tsaye wajen bayar da kwangila.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

Okorie ya bayyana cewa kwamitin aiwatar da ayyukan da ya jagoranta ya gano rashin jituwa a lokacin da ake sa ido kan ayyukan musamman a filin jirgin saman Katsina, inda babu wani ɗan kwangila da yake gudanar da aiki ciki har da Al-Duraq, duk da cewa akwai sunayensu matsayin ƴan kwangila.

Ya shaida cewar har ya kammala aikin gwamnati a watan Mayun 2023, ba a aiwatar da aikin kwangilar da kamfanin Al-Duraq ba wacce ta kai Naira miliyan 800. Ya ƙara da cewa, yana da masaniyar wani kuɗi da aka biya wa Al-Duraq kashi 30 cikin 100 na tara kuɗaɗen shiga, amma babu hannun shi cikin tsarin biyan kuɗi wanda aka yi shi bisa ƙa’ida ba.

Kanu Agabi, SAN, Lauyan Sirika, ya buƙaci da a ɗage zaman domin duba takardun ƙarar, buƙatar da wasu lauyoyin masu ƙara suka goyi bayan kuma masu gabatar da ƙara ba su yi hamayya ba.

Sakamakon haka, Mai shari’a Sylvanus Oriji ya ɗage sauraron ƙarar har zuwa ranar 30 ga wata domin yi masa tambayoyi da kuma ci gaba da shari’ar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CourtEFCCHadi SirikaNAAFPolice
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masana’antun Samar Da Kayayyakin Masarufi Na Gudana Cikin Wani Yanayi Mai Armashi A Kasar Sin

Next Post

Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Sin: Ana Kokarin Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa A Nahiyar Asiya

Related

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

4 days ago
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

1 month ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

1 month ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

3 months ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

4 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

4 months ago
Next Post
Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Sin: Ana Kokarin Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa A Nahiyar Asiya

Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Sin: Ana Kokarin Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa A Nahiyar Asiya

LABARAI MASU NASABA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

July 9, 2025
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

July 9, 2025
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

July 9, 2025
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

July 9, 2025
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

July 9, 2025
Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

July 9, 2025
Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

July 8, 2025
Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

July 8, 2025
Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

July 8, 2025
Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo

Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo

July 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.