• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Rufe Masallatai Mataki Ne Na Haifar Da Rudani

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Zargin Rufe Masallatai Mataki Ne Na Haifar Da Rudani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun da jimawa, mun sha ji, da ganin rahotanni dake zargin cewa wai mahukunta a kasar Sin na rushe masallatai, ko mayar da su wuraren aikata wasu harkoki na daban. Irin wadannan rahotanni da wasu kafofin watsa labaran yammacin duniya ke yadawa na da matukar hadari, kasancewar suna kunshe da zarge-zarge marasa tushe, da karairayi marasa shaidu na zahiri.

A baya bayan nan, wata kafar watsa labarai ta yammacin duniya ta rawaito zargin da hukumar kare hakkin dan’adam ta “Human Right Watch” ko HRW ta yi, cewa wai ana samun karuwar ruguza tsarin addinai a shekarun baya-bayan nan a kasar Sin, kuma wai Sin na kara azamar neman karfin iko kan addinai.

  • Gwamnan Bauchi Ya Gabatar Da Biliyan 300 A Matsayin Kasafin Kudin 2024
  • Kwace Wa NNPP Zaben Kano Na Iya Haddasa Tashin Hankali A Afrika – NNPP

Cikin wannan zargi akwai abubuwan lura da yawa, amma kadan daga cikinsu akwai batun rashin shaidu na hakika, ko korafi daga musulmin kasar dake zaune a wuraren da aka yi zargin. Wato dai idan har HRW na da gaskiya kan zargin da ta yi, kamata ya yi ta bayyana shaidun gani da ido, ba wai cewa wai “An gano daga hotunan tauraron dan Adam” ba!

Kaza lika da yake rahoton na HRW ya ce mahukuntan Sin na kokarin samun karin iko kan addinai, ba wai addinin musulunci kadai ba, abun tambayar shi ne wane irin iko ne Sin za ta samu idan ta dakile addinai da mabiyansu?

Ga duk mai son sanin ainihin gaskiyar halin da musulmi, da mabiya sauran addinai suke ciki a kasar Sin, hanya daya mafi sauki ita ce ya bibiyi rahotanni daga mazauna kasar, ko dai Sinawa ’yan kasa, ko baki mazauna kasar dake neman ilimi, ko gudanar da harkokin kasuwanci da sauransu, wadanda za su fadi gaskiyar lamari bisa abubuwan da suka gani da idanun su, ba wai jita-jita daga kafofin dake adawa da ci gaban kasar Sin ba.

Labarai Masu Nasaba

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Ko shakka babu kasar Sin na da tsare-tsare daban daban na kare kima, da martabar addinai, da hakkokin mabiya addinai bisa doka. Alal misali, a ranar 3 ga watan Afirilun shekarar 2018, ofishin watsa labarai na majalissar gudanarwar kasar Sin, ya fitar da takardar bayanai mai taken Manufofi da ayyukan Sin na kare ’yancin bin addinai”, wadda a ciki aka zayyana matakan da kasar ke bi na tabbatar da kowa ya yi addinin da ya zaba bisa radin kansa, da tabbatar da zaman jituwa tsakanin mabiya addinai daban daban, da ma wadanda ba sa bin kowane addini.

Kaza lika, takardar ta yi bayani filla-filla, game da matakan da Sin ke bi na tabbatar da an martaba ikon mabiya addinai na yin ibada ba tare da tsangwama ba, da inganta wuraren ibada, ta yadda mabiya addinai da wadanda ba sa bin kowane addini za su rayu cikin jituwa.

A nan birnin Beijing ga misali, akwai gwamman masallatai dake sassan gundumomin birnin daban daban, wadanda musulmi ke amfani da su a ko da yaushe don gudanar da ibada, kuma tsawon sama da shekaru 10 da nake halartar masallatan dake cikin birnin, ban taba ji ko ganin an rushe wani masallaci ba! Hakan ya tabbatar min da cewa akwai wasu boyayyu, kuma munanan manufofi, a zukatan masu kitsawa, da yada jita-jitar rushe masallatai a Sin.

Daga karshe akwai bukatar mu rika taka-tsantan da kafofin dake yada labaran karya domin cimma burin siyasa. Domin ko ba komai, sauraro da aiki da irin wadannan labarai na bogi, na iya haifar da rashin jituwa, da tada hankulan al’umma, da haifar da tashe-tashen hankula, musamman a irin wannan lokaci da duniya ta fi bukatar hadin kai, da zaman lafiya sama da kowane lokaci a tarihi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kasar SinXianjingXin hua
ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Ɗumi-Ɗumi: Jam’iyyar APC Ta Kori Shugabanta Na Jihar Bauchi, Aliyu Misau

Next Post

Bikin CISCE Ya Jawo Hankalin Kamfanonin Amurka Da Kasashen Turai

Related

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

26 minutes ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

2 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

3 hours ago
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

19 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

19 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

21 hours ago
Next Post
Bikin CISCE Ya Jawo Hankalin Kamfanonin Amurka Da Kasashen Turai

Bikin CISCE Ya Jawo Hankalin Kamfanonin Amurka Da Kasashen Turai

LABARAI MASU NASABA

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Masallatai

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.