ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Rufe Masallatai Mataki Ne Na Haifar Da Rudani

by CGTN Hausa
2 years ago
Masallatai

Tun da jimawa, mun sha ji, da ganin rahotanni dake zargin cewa wai mahukunta a kasar Sin na rushe masallatai, ko mayar da su wuraren aikata wasu harkoki na daban. Irin wadannan rahotanni da wasu kafofin watsa labaran yammacin duniya ke yadawa na da matukar hadari, kasancewar suna kunshe da zarge-zarge marasa tushe, da karairayi marasa shaidu na zahiri.

A baya bayan nan, wata kafar watsa labarai ta yammacin duniya ta rawaito zargin da hukumar kare hakkin dan’adam ta “Human Right Watch” ko HRW ta yi, cewa wai ana samun karuwar ruguza tsarin addinai a shekarun baya-bayan nan a kasar Sin, kuma wai Sin na kara azamar neman karfin iko kan addinai.

  • Gwamnan Bauchi Ya Gabatar Da Biliyan 300 A Matsayin Kasafin Kudin 2024
  • Kwace Wa NNPP Zaben Kano Na Iya Haddasa Tashin Hankali A Afrika – NNPP

Cikin wannan zargi akwai abubuwan lura da yawa, amma kadan daga cikinsu akwai batun rashin shaidu na hakika, ko korafi daga musulmin kasar dake zaune a wuraren da aka yi zargin. Wato dai idan har HRW na da gaskiya kan zargin da ta yi, kamata ya yi ta bayyana shaidun gani da ido, ba wai cewa wai “An gano daga hotunan tauraron dan Adam” ba!

ADVERTISEMENT

Kaza lika da yake rahoton na HRW ya ce mahukuntan Sin na kokarin samun karin iko kan addinai, ba wai addinin musulunci kadai ba, abun tambayar shi ne wane irin iko ne Sin za ta samu idan ta dakile addinai da mabiyansu?

Ga duk mai son sanin ainihin gaskiyar halin da musulmi, da mabiya sauran addinai suke ciki a kasar Sin, hanya daya mafi sauki ita ce ya bibiyi rahotanni daga mazauna kasar, ko dai Sinawa ’yan kasa, ko baki mazauna kasar dake neman ilimi, ko gudanar da harkokin kasuwanci da sauransu, wadanda za su fadi gaskiyar lamari bisa abubuwan da suka gani da idanun su, ba wai jita-jita daga kafofin dake adawa da ci gaban kasar Sin ba.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Ko shakka babu kasar Sin na da tsare-tsare daban daban na kare kima, da martabar addinai, da hakkokin mabiya addinai bisa doka. Alal misali, a ranar 3 ga watan Afirilun shekarar 2018, ofishin watsa labarai na majalissar gudanarwar kasar Sin, ya fitar da takardar bayanai mai taken Manufofi da ayyukan Sin na kare ’yancin bin addinai”, wadda a ciki aka zayyana matakan da kasar ke bi na tabbatar da kowa ya yi addinin da ya zaba bisa radin kansa, da tabbatar da zaman jituwa tsakanin mabiya addinai daban daban, da ma wadanda ba sa bin kowane addini.

Kaza lika, takardar ta yi bayani filla-filla, game da matakan da Sin ke bi na tabbatar da an martaba ikon mabiya addinai na yin ibada ba tare da tsangwama ba, da inganta wuraren ibada, ta yadda mabiya addinai da wadanda ba sa bin kowane addini za su rayu cikin jituwa.

A nan birnin Beijing ga misali, akwai gwamman masallatai dake sassan gundumomin birnin daban daban, wadanda musulmi ke amfani da su a ko da yaushe don gudanar da ibada, kuma tsawon sama da shekaru 10 da nake halartar masallatan dake cikin birnin, ban taba ji ko ganin an rushe wani masallaci ba! Hakan ya tabbatar min da cewa akwai wasu boyayyu, kuma munanan manufofi, a zukatan masu kitsawa, da yada jita-jitar rushe masallatai a Sin.

Daga karshe akwai bukatar mu rika taka-tsantan da kafofin dake yada labaran karya domin cimma burin siyasa. Domin ko ba komai, sauraro da aiki da irin wadannan labarai na bogi, na iya haifar da rashin jituwa, da tada hankulan al’umma, da haifar da tashe-tashen hankula, musamman a irin wannan lokaci da duniya ta fi bukatar hadin kai, da zaman lafiya sama da kowane lokaci a tarihi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

November 17, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95
Daga Birnin Sin

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku
Daga Birnin Sin

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Next Post
Bikin CISCE Ya Jawo Hankalin Kamfanonin Amurka Da Kasashen Turai

Bikin CISCE Ya Jawo Hankalin Kamfanonin Amurka Da Kasashen Turai

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

November 17, 2025
Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

November 17, 2025
Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

November 17, 2025
Tsohuwar Firaministan Bangaladesh Sheikha Hasina,

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025
Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

November 17, 2025
Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

November 17, 2025
Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.