• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Yi Wa Almajiri Fyade: Masu Kare Hakkin Dan’adam Sun Sake Shigar Da Kara

by Abubakar Abba
8 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Kotu Ta Hana Miji Magana Da Matarsa Tsawon Mako Biyu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu masu kare hakkin ‘yan Adam a Jihar Kaduna sun shigar da kara a gaban kotun Majistari da ke da zama a titin Daura Road, mai lamba 37.

Sun shigar da karar ce, don kotun ta sake bude shari’ar yaron nan Almajiri dan shekara 13 da wani mai suna Isah Abdullah daya daga cikin hadimin ‘yar majalsair dokin jihar Kaduna Munirat Suleiman mai wakilitar mazabar Saminaka ya yi wa fyade.

  • Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Danyen Aikin Dake Barazanar Jefa Yankin Cikin Wani Bala’i
  • Xi Ya Jaddada Ba Da Cikakkiyar Dama Ga Fa’idar Siyasa Ta CPPCC

A cewasu, ba su amince da wancan hukukuncin da alkalin kotun Majistari mai lamba 2 Mai Shari’a Aliyu Dogara ya yanke na wanke Isah Abdullah da kuma sakinsa ba.

Idan za a iya tunawa, binciken da sashin manyan laifuka na rundunar ‘yansandan a Jihar Kaduna ya yi, a kan zargin ya gabatar da Isa gaban kotun mai lamba 2, wanda kotun ta bayar da umarni a ajiye Isah a gidan gyaran hali na jihar, kafin ma’aikatar Shari’ar jihar ta bayar da shawara a kan zargin.

Amma bayan jiran shawara daga ma’aikatar Shara’a ta jihar, ta wanke Isa a sakamakon rahoton gwaji da aka samu daga Asibiti a Saminaka da kuma Asibitin koyarwa na Barau Dikko.

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

Sai dai, masu kare rajin hakkin ‘yan’adam a jihar, sun bayyana cewa, ba su amince da wancan hukuncin kotun da kuma takardun gwajin lafiyar yaron da Asibitin Barau Dikko da Garin Saminaka suka yi a kan Almajirin ba, inda suka sake garzayawa kotun ta Majistari da ke mai lamba 37, don ta bude Shari’ar.

A hirarsa da ‘yan jarida a Kaduna daya daga cikin masu kare rajin Marwan Yabo ya ce, wancan hukuncin da kotun Daura Road mai lamba 2 ta yanke bamu yarda da shi ba.

A cewarsa, masu kare wanda ake zargin a gaban kotun, sun yi amfani da wasu takardun da aka yiwa yaron gwaji ne, a wani Asibiti da ke a Saminaka da kuma gwajin da aka yi, a Asibitin Barau Dikko, kuma takardun gwajin da aka yi, a wadannan Asibitocin biyu, na hannun mu.

Ya ci gaba da cewa, akwai kuma wasu takardu biyu wadanda suke nuna cewa, wai daga Asibitin Saminaka da kuma na Barau Dikko ne, aka bayar.

Ya kara da cewa, “To amma bamu san yadda aka yi suka samo wadannan takardun biyu ba, domin Asibitin Barau Dikko, a baya da kansu ne suka yi wa yaron gwaji suka kuma tura shi zuwa Asibitin kashi na Dala, da ke a Kano don a yi wa yaron aiki”.

Ya ce, bayan kotun mai lamba 2 ta bayar da umarnin cewa, a ajiye Isah a gidan gyran hali na jihar har sai yaron ya samu lafiya kafin a fara shari’ar, sai kawai muka ji cewa, wai kotun mai lamba 2 ta wanke Isah daga zargin, alhali ba a ma fara shariar gadan-gadan ba, kuma ba ji ta bakin yaron a kan me ya faru ba.

Shi ma daya mai kare hakiin ‘yan’adam kuma lauyan yaron Barista Sani Shehu a zantawarsa da ‘yanjarida ya ce, za su tabbatar an binciki wancan hukuncin da kotun mai lamba 2 ta yanke, inda ya kara da cewa,”Muna zargin akwai shubuha a cikin hukuncin da kotun mai lamba 2 ta yanke”.

Ya ce, idan har ita ma’aikatar shari’a ta kamar yadda takardun suka nuna cewa, ta dogara ne da wasu takardu na likita wadanda mai yiwuwa, wadancan takardun na likitan an kawo su ne ta bayan fage, ma’aikatar kuma ta yi abin da ta yi, doka ta bamu damar muma mu sake bude wata sabuwar shari’a.

Ya ce, ita kuma kotun da ta wanke wanda ake zargin, “Muna da ikon mu nemi kotu ta sama, ta warware wancan hukuncin na kotun ta 2, don a sake wani bincike don mu gabatar da dalilanmu”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FyadeKadunaKotu
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gurfanar Da Tsohon Alkali A Kotu Kan Zargin Lakada Wa Matar Aure Duka

Next Post

Matafiyi Obobo Ya Rasu

Related

Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

4 weeks ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

2 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

2 months ago
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

2 months ago
Rikita-rikitar Da Ta Biyo Bayan Mutuwar Mawaki Mohbad
Kotu Da Ɗansanda

MohBad: Nurse Za Ta Fuskanci Shari’a, Sannan Kotu Ta Wanke Naira Marley, Sam Larry Da PrimeBoy

2 months ago
‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja

3 months ago
Next Post
Matafiyi Obobo Ya Rasu

Matafiyi Obobo Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.