• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ziyarar Ministan Wajen Sin A Afirka: Zumunci Mai Dadi Ba Irin Na ’Yan Ta-more Ba

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ziyarar Ministan Wajen Sin A Afirka: Zumunci Mai Dadi Ba Irin Na ’Yan Ta-more Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ziyarar ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi, a wasu kasashen Afirka a farkon 2024 kusan al’ada ce da ministocin harkokin wajen kasar kan yi a farkon kowace shekara cikin shekaru 34 a jere.

Irin wannan ziyara da kasar Sin ke yi a farkon shekara tun daga 1991 ta haifar da da mai ido ga Afirka idan aka yi la’akari da yadda aka raya zumuncin aiki da cin gajiyar juna tare da fuskantar kalubalen siyasar duniya domin a gudu tare a tsira tare.

  • Nijeriya Na Fatan Samun Karin Masu Zuba Jari A Taron Kasuwanci Na Duniya
  • Matsafa Sun Sare Kan Budurwa A Adamawa

Duk dan Afirka da ya samu wayewar zamani, har yau mulkin mallakar da Turawan yamma suka yi wa Afirka yana masa daci a rai saboda bautarwa da azabtarwa da kakanninmu suka sha a hannunsu. Wannan ya sa duk lokacin da na yi la’akari da huldar kasuwancin da ke tsakanin Afirka da Sin da sauran harkoki sai na kara fahimtar hujjojin kasashenmu na rungumar Sin.

Ziyarar minista Wang Yi, ta karfafa neman goyon bayan Afirka a kan kudurin Sin na kawo ci gaba ga juna a duniya, da tabbatar da ’yanci da tsaro da kuma wayewar kai ta bai-daya da za ta kawo alheri ga kowa da kowa. Irin yanayin da duniya ke ciki yanzu hatta jaririn da ba a haifa ba ya san akwai matsala saboda rashin mutunta hakkin bil’adama da yaudara da rashin mutunta kasashe masu tasowa daga Turawan yamma masu da’awar jagorancin duniya. Abin da Isra’ila ke yi bisa goyon bayan Amurka a yankin Gaza ya nuna hakan baro-baro a fili.

Don haka, Afirka ta yi ma kanta kiyamullaili ta rungumi hulda da Sin domin samun ci gaba. Abin jinjina ne yadda kasashen Afirka 52 suka rattaba hannu a kan yarjeniyoyin tsarin Ziri Daya da Hanya Daya na biliyoyin daloli don samar wa kansu da ababen more rayuwa kamar titunan mota, layukan jirgin kasa, tashoshin teku da sauran abubuwan da ake bukata na bunkasa tattalin arzikin.

Labarai Masu Nasaba

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

A lokacin da minista Wang Yi ya isa kasar Masar, ya nuna cewa kasar Sin tana goyon bayan adalci ga kowa a duniya musamman kan yakin zirin Gaza wanda ya fara fantsama tare da kai hari a kan jiragen ruwa a tekun Bahar Maliya.

A tattaunawarsa da shugaban Tunisiya Kais Saied, Wang Yi ya bayyana yadda kyakkawar alaka ta dore a tsakanin kasashen biyu na tsawon shekara 60 tare da jaddada ci gaba da kawance ta fannonin raya kasa da bunkasar tattalin arziki. Shugaban Tunisiya a nasa bangaren ya jaddada goyon kasar Sin a matsayin kasa daya dunkulalliya tare da yabawa da irin nasarorin da take samu ta fuskar ci gaban zamani.

A kasar Togo, minista Wang Yi ya samu kyakkyawar tarba daga takwaransa na kasar, Robert Dussey inda kasar ta Togo ta sake nanata goyon baya ga Sin musamman kan ci gaba da zaman yankin Taiwan a cikinta. Tana mai cewa kasar Sin kwaya daya ce kwallin kwal a duniya.

A kasar Cote d’Ivoire kuwa inda minista Wang Yi ya yada zango na karshe a ziyarar tasa, ya samu tabbaci daga shugaban kasar, Alassane Ouattara cewa ya yi, kasarsa ba ta da babbar kawa ta cinikayya da zuba jari kamar Sin, don haka za ta ci gaba da kyautata zumuncin da ke tsakaninsu. Abin alfahari ba ga Cote d’Ivoire ba kawai har da sauran kasashen Afirka, minista Wang ya ce Sin za ta ci gaba da inganta tsarin cin moriyar juna da Afirka da kuma taimakon kasashen yankin wajen aiki da tsare-tsare mafi kyau da suka fi dacewa da su ta yadda za su ci gajiyar albarkatun da suke da su yadda ya kamata.

Wannan ziyara da minista Wang Yi ya kawo Afirka, ta sake bai wa yankin damar ci gaba da kulla alakar cinikayya mai gwabi a tsakaninsu. Yana da matukar karfafa gwiwa ga kasashen Afirka bisa yadda Sin take samun bunkasar tattalin arziki. Alkaluman da aka fitar na shekarar 2023 sun nuna hada-hadar tattalin arzikinta sun haura fiye da Yuan tiriliyan 126, da ke nufin ta samu ci gaba da kashi 5.2 cikin dari a kan wanda ta samu a shekarar 2022.

Irin wannan ziyara ta ministan wajen Sin, za ta kara bude hanyoyin da Afirka za ta bi sawun Sin ta fannin kere-kere da kirkire-kirkire da zamanantar da kasashensu.

A wata ziyara da na kai shalkwatar Kamfanin China Harbour Engineering Company da ke Nijeriya a Unguwar Maitama, Abuja a wannan Alhamis din, Manajan Daraktan Kamfanin a Nijeriya, Mista Jason Wang ya bayyana min yadda suka kammala aikin titin Keffi (a Jihar Nasarawa) zuwa Makurdi (a Jihar Benue) da kuma kokarin da suke yi na karasa kashi na biyu na aikin wanda zai hade Makurdi da Enugu. Haka nan mun yi magana a kan tashar tekun da kamfaninsu ya samar a Legas ta Lekki wacce za ta samar da dubban aikin yi da biliyoyin kudin shiga ga Nijeriya.

Duk irin wadannan kyawawan abubuwa sun faru ne sakamakon martaba juna a tsakanin Sin da Afirka, ba kamar Turawan yamma da suka zama ’yan ta-more ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfirkaAlakar Sin da AfirkaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sake Fasalin Naira Ya Taimaka Wajen Samun  Ingantaccen Zabe A 2023 —Buhari Ya Jaddada

Next Post

Xi Jinping Ya Bada Muhimmin Umarni A Wajen Bikin Bayar Da Lambar Yabo Ta Injiniya Ta Kasa

Related

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
Daga Birnin Sin

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

3 minutes ago
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

17 hours ago
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya
Daga Birnin Sin

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

18 hours ago
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

19 hours ago
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

20 hours ago
An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

21 hours ago
Next Post
Xi Jinping Ya Bada Muhimmin Umarni A Wajen Bikin Bayar Da Lambar Yabo Ta Injiniya Ta Kasa

Xi Jinping Ya Bada Muhimmin Umarni A Wajen Bikin Bayar Da Lambar Yabo Ta Injiniya Ta Kasa

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

September 15, 2025
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

September 15, 2025
Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

September 15, 2025
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

September 15, 2025
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

September 15, 2025
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

September 15, 2025
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.