ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ziyarar Mr. Wang Yi A Afirka Ta Kafa Tarihi

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
Wang yi

A makon da ya gabata ne, ministan harkokin wajen kasar Sin, Mr. Wang Yi, ya kammala ziyararsa a wasu kasashen Afirka da suka hada da Namibia, Jamhuriyar Congo, Chadi da kuma Nijeriya.

Mr. Wang ya samu kyakkyawar marhabin a wadannan kasashe da ya ziyarta. Kuma wannan ziyara tashi tana matsayin kara jaddada manufar taron kolin nan da aka gudanar a birnin Beijing a shekarar da ta gabata tsakanin Sin da kasashen Afirka, inda aka cimma yarjejeniyar cude-ni- in-cude-ka, wato tsakanin Sin da kawayenta kasashen Afirka.

  • Gwamnan Zamfara Ya Yaba Wa Rundunar Tsaro Tare Da Jajanta Wa Al’ummar Da Harin Jirgin Sojin Ya Shafa A Jihar
  • Daga Cikon Benci Zuwa Cikakken Jarumin Kannywood – Abubakar Waziri

Babu shakka wannan ziyara ta Mr. Wang Yi ta kara zurfafa dangantaka tsakanin Sin da Afirka, musamman idan aka yi la’akari da cewa irin wannan ziyara ba ta da nasaba da yunkurin tsoma baki a cikin harkokin gida na kasashen Afirka, illa iyakar kokarin duba hanyoyin da Sin za ta bada gudummawarta wajen bunkasa harkokin tattalin arziki, cinikayya, al’adu, tsaro, kimiyya da fasaha, wato kamar dai yadda ministan harkokin wajen na Sin ya jaddada a ziyarar tasa, har ma ya kara da cewa Sin za ta tallafawa Nijeriya a sha’anin yaki da ta’addanci, bayar da kariya da tsaro ga zaman lafiya da kuma goyawa Nijeriya baya wajen ganin tana taka muhimmiyar rawa a cikin harkokin kasa da kasa.

ADVERTISEMENT

Matakin da Bankin Raya Kasa na Sin (CDB) ya dauka game da batun samar da zunzurutun kudi har dala miliyan 254 da digo 76 (kwatankwacin dalar Amurka miliyan 254.76) domin ci gaba da aiwatar da aikin layin dogo a Nijeriya, ya kara tabbatar da gaskiyar kalaman Mr. Wang na cewa China tana daukar batutuwan da suka shafi kasashen Afirka da muhimmanci.

Shi dai wannan layin dogo mai tsawon kilomita 203, wanda zai sada biranen Kano da Kaduna, idan aka kammala shi zai taimaka wajen bunkasa harkokin zirga-zirgar jama’a, sannan kuma zai habaka harkokin tattalin arziki a yankin ta hanyar kafa masana’antu, abin da zai samar da aikin yi ga dimbin jama’a.

LABARAI MASU NASABA

Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka

CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

Abin lura a nan shi ne, zabar kasashen Afirka da ministocin harkokin wajen na kasar Sin suka saba yi a matsayin kasashen da za su fara kaiwa ziyara a cikin farkon shekara ya kara jaddada muhimmancin da kasar Sin take baiwa kawayenta kasashen Afirka. Dama dai China da Nijeriya sun dade suna cudanya da juna, suna mutunta juna kuma suna goyon bayan juna a muhimman batutuwa na kasa da kasa. Sabo da haka wannan ziyara ta Mr. Wang Yi ta kara zurfafa kyakkyawar dangantaka tsakanin kasashen biyu. (Lawal Mamuda)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka

November 12, 2025
CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 
Ra'ayi Riga

CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

November 11, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Raba Kayan Makaranta Kyauta Ga Dalibai 789,000

Gwamnatin Kano Ta Raba Kayan Makaranta Kyauta Ga Dalibai 789,000

LABARAI MASU NASABA

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025
Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

November 17, 2025
Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

November 17, 2025
Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.