• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ziyarar Mr. Wang Yi A Afirka Ta Kafa Tarihi

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Ziyarar Mr. Wang Yi A Afirka Ta Kafa Tarihi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A makon da ya gabata ne, ministan harkokin wajen kasar Sin, Mr. Wang Yi, ya kammala ziyararsa a wasu kasashen Afirka da suka hada da Namibia, Jamhuriyar Congo, Chadi da kuma Nijeriya.

Mr. Wang ya samu kyakkyawar marhabin a wadannan kasashe da ya ziyarta. Kuma wannan ziyara tashi tana matsayin kara jaddada manufar taron kolin nan da aka gudanar a birnin Beijing a shekarar da ta gabata tsakanin Sin da kasashen Afirka, inda aka cimma yarjejeniyar cude-ni- in-cude-ka, wato tsakanin Sin da kawayenta kasashen Afirka.

  • Gwamnan Zamfara Ya Yaba Wa Rundunar Tsaro Tare Da Jajanta Wa Al’ummar Da Harin Jirgin Sojin Ya Shafa A Jihar
  • Daga Cikon Benci Zuwa Cikakken Jarumin Kannywood – Abubakar Waziri

Babu shakka wannan ziyara ta Mr. Wang Yi ta kara zurfafa dangantaka tsakanin Sin da Afirka, musamman idan aka yi la’akari da cewa irin wannan ziyara ba ta da nasaba da yunkurin tsoma baki a cikin harkokin gida na kasashen Afirka, illa iyakar kokarin duba hanyoyin da Sin za ta bada gudummawarta wajen bunkasa harkokin tattalin arziki, cinikayya, al’adu, tsaro, kimiyya da fasaha, wato kamar dai yadda ministan harkokin wajen na Sin ya jaddada a ziyarar tasa, har ma ya kara da cewa Sin za ta tallafawa Nijeriya a sha’anin yaki da ta’addanci, bayar da kariya da tsaro ga zaman lafiya da kuma goyawa Nijeriya baya wajen ganin tana taka muhimmiyar rawa a cikin harkokin kasa da kasa.

Matakin da Bankin Raya Kasa na Sin (CDB) ya dauka game da batun samar da zunzurutun kudi har dala miliyan 254 da digo 76 (kwatankwacin dalar Amurka miliyan 254.76) domin ci gaba da aiwatar da aikin layin dogo a Nijeriya, ya kara tabbatar da gaskiyar kalaman Mr. Wang na cewa China tana daukar batutuwan da suka shafi kasashen Afirka da muhimmanci.

Shi dai wannan layin dogo mai tsawon kilomita 203, wanda zai sada biranen Kano da Kaduna, idan aka kammala shi zai taimaka wajen bunkasa harkokin zirga-zirgar jama’a, sannan kuma zai habaka harkokin tattalin arziki a yankin ta hanyar kafa masana’antu, abin da zai samar da aikin yi ga dimbin jama’a.

Labarai Masu Nasaba

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

Abin lura a nan shi ne, zabar kasashen Afirka da ministocin harkokin wajen na kasar Sin suka saba yi a matsayin kasashen da za su fara kaiwa ziyara a cikin farkon shekara ya kara jaddada muhimmancin da kasar Sin take baiwa kawayenta kasashen Afirka. Dama dai China da Nijeriya sun dade suna cudanya da juna, suna mutunta juna kuma suna goyon bayan juna a muhimman batutuwa na kasa da kasa. Sabo da haka wannan ziyara ta Mr. Wang Yi ta kara zurfafa kyakkyawar dangantaka tsakanin kasashen biyu. (Lawal Mamuda)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Kai Sabon Matsayi A Shekarar 2024

Next Post

Gwamnatin Kano Ta Raba Kayan Makaranta Kyauta Ga Dalibai 789,000

Related

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!
Ra'ayi Riga

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

6 days ago
Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne
Ra'ayi Riga

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

6 days ago
Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?
Ra'ayi Riga

Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?

1 week ago
Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba
Ra'ayi Riga

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

2 weeks ago
Manufar Raya Biranen Kasar Sin: Ba Wai Kawai a Tabbatar Da “Tsayi” Ba Ne Har Ma Da “Zafi”
Ra'ayi Riga

Manufar Raya Biranen Kasar Sin: Ba Wai Kawai a Tabbatar Da “Tsayi” Ba Ne Har Ma Da “Zafi”

2 weeks ago
Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba
Ra'ayi Riga

Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

2 weeks ago
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Raba Kayan Makaranta Kyauta Ga Dalibai 789,000

Gwamnatin Kano Ta Raba Kayan Makaranta Kyauta Ga Dalibai 789,000

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Nijeriya Sun Yi Ta’aziyyar Waɗanda Suka Rasu A Ambaliyar Ruwa A Adamawa

Gwamnonin Nijeriya Sun Yi Ta’aziyyar Waɗanda Suka Rasu A Ambaliyar Ruwa A Adamawa

July 29, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Naɗa Abdulkadir Ibrahim A Matsayin Sabon Sarkin Katsinan Gusau Na 16

Gwamnan Zamfara Ya Naɗa Abdulkadir Ibrahim A Matsayin Sabon Sarkin Katsinan Gusau Na 16

July 29, 2025
Tsohon Ɗan Takarar Mataimakin Gwamnan Kaduna Na PDP Ya Koma ADC

Tsohon Ɗan Takarar Mataimakin Gwamnan Kaduna Na PDP Ya Koma ADC

July 29, 2025
EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom

EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom

July 29, 2025
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

July 29, 2025
An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

July 28, 2025
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

July 28, 2025
Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

July 28, 2025
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

July 28, 2025
An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

July 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.