• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ziyarar Mr. Wang Yi A Afirka Ta Kafa Tarihi

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Ziyarar Mr. Wang Yi A Afirka Ta Kafa Tarihi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A makon da ya gabata ne, ministan harkokin wajen kasar Sin, Mr. Wang Yi, ya kammala ziyararsa a wasu kasashen Afirka da suka hada da Namibia, Jamhuriyar Congo, Chadi da kuma Nijeriya.

Mr. Wang ya samu kyakkyawar marhabin a wadannan kasashe da ya ziyarta. Kuma wannan ziyara tashi tana matsayin kara jaddada manufar taron kolin nan da aka gudanar a birnin Beijing a shekarar da ta gabata tsakanin Sin da kasashen Afirka, inda aka cimma yarjejeniyar cude-ni- in-cude-ka, wato tsakanin Sin da kawayenta kasashen Afirka.

  • Gwamnan Zamfara Ya Yaba Wa Rundunar Tsaro Tare Da Jajanta Wa Al’ummar Da Harin Jirgin Sojin Ya Shafa A Jihar
  • Daga Cikon Benci Zuwa Cikakken Jarumin Kannywood – Abubakar Waziri

Babu shakka wannan ziyara ta Mr. Wang Yi ta kara zurfafa dangantaka tsakanin Sin da Afirka, musamman idan aka yi la’akari da cewa irin wannan ziyara ba ta da nasaba da yunkurin tsoma baki a cikin harkokin gida na kasashen Afirka, illa iyakar kokarin duba hanyoyin da Sin za ta bada gudummawarta wajen bunkasa harkokin tattalin arziki, cinikayya, al’adu, tsaro, kimiyya da fasaha, wato kamar dai yadda ministan harkokin wajen na Sin ya jaddada a ziyarar tasa, har ma ya kara da cewa Sin za ta tallafawa Nijeriya a sha’anin yaki da ta’addanci, bayar da kariya da tsaro ga zaman lafiya da kuma goyawa Nijeriya baya wajen ganin tana taka muhimmiyar rawa a cikin harkokin kasa da kasa.

Matakin da Bankin Raya Kasa na Sin (CDB) ya dauka game da batun samar da zunzurutun kudi har dala miliyan 254 da digo 76 (kwatankwacin dalar Amurka miliyan 254.76) domin ci gaba da aiwatar da aikin layin dogo a Nijeriya, ya kara tabbatar da gaskiyar kalaman Mr. Wang na cewa China tana daukar batutuwan da suka shafi kasashen Afirka da muhimmanci.

Shi dai wannan layin dogo mai tsawon kilomita 203, wanda zai sada biranen Kano da Kaduna, idan aka kammala shi zai taimaka wajen bunkasa harkokin zirga-zirgar jama’a, sannan kuma zai habaka harkokin tattalin arziki a yankin ta hanyar kafa masana’antu, abin da zai samar da aikin yi ga dimbin jama’a.

Labarai Masu Nasaba

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

Abin lura a nan shi ne, zabar kasashen Afirka da ministocin harkokin wajen na kasar Sin suka saba yi a matsayin kasashen da za su fara kaiwa ziyara a cikin farkon shekara ya kara jaddada muhimmancin da kasar Sin take baiwa kawayenta kasashen Afirka. Dama dai China da Nijeriya sun dade suna cudanya da juna, suna mutunta juna kuma suna goyon bayan juna a muhimman batutuwa na kasa da kasa. Sabo da haka wannan ziyara ta Mr. Wang Yi ta kara zurfafa kyakkyawar dangantaka tsakanin kasashen biyu. (Lawal Mamuda)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Kai Sabon Matsayi A Shekarar 2024

Next Post

Gwamnatin Kano Ta Raba Kayan Makaranta Kyauta Ga Dalibai 789,000

Related

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
Ra'ayi Riga

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

1 day ago
Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa
Ra'ayi Riga

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

2 days ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

3 days ago
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

1 week ago
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
Ra'ayi Riga

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

2 weeks ago
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Ra'ayi Riga

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

2 weeks ago
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Raba Kayan Makaranta Kyauta Ga Dalibai 789,000

Gwamnatin Kano Ta Raba Kayan Makaranta Kyauta Ga Dalibai 789,000

LABARAI MASU NASABA

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

July 5, 2025
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.