ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ziyarar Mr. Wang Yi A Afirka Ta Kafa Tarihi

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Wang yi

A makon da ya gabata ne, ministan harkokin wajen kasar Sin, Mr. Wang Yi, ya kammala ziyararsa a wasu kasashen Afirka da suka hada da Namibia, Jamhuriyar Congo, Chadi da kuma Nijeriya.

Mr. Wang ya samu kyakkyawar marhabin a wadannan kasashe da ya ziyarta. Kuma wannan ziyara tashi tana matsayin kara jaddada manufar taron kolin nan da aka gudanar a birnin Beijing a shekarar da ta gabata tsakanin Sin da kasashen Afirka, inda aka cimma yarjejeniyar cude-ni- in-cude-ka, wato tsakanin Sin da kawayenta kasashen Afirka.

  • Gwamnan Zamfara Ya Yaba Wa Rundunar Tsaro Tare Da Jajanta Wa Al’ummar Da Harin Jirgin Sojin Ya Shafa A Jihar
  • Daga Cikon Benci Zuwa Cikakken Jarumin Kannywood – Abubakar Waziri

Babu shakka wannan ziyara ta Mr. Wang Yi ta kara zurfafa dangantaka tsakanin Sin da Afirka, musamman idan aka yi la’akari da cewa irin wannan ziyara ba ta da nasaba da yunkurin tsoma baki a cikin harkokin gida na kasashen Afirka, illa iyakar kokarin duba hanyoyin da Sin za ta bada gudummawarta wajen bunkasa harkokin tattalin arziki, cinikayya, al’adu, tsaro, kimiyya da fasaha, wato kamar dai yadda ministan harkokin wajen na Sin ya jaddada a ziyarar tasa, har ma ya kara da cewa Sin za ta tallafawa Nijeriya a sha’anin yaki da ta’addanci, bayar da kariya da tsaro ga zaman lafiya da kuma goyawa Nijeriya baya wajen ganin tana taka muhimmiyar rawa a cikin harkokin kasa da kasa.

ADVERTISEMENT

Matakin da Bankin Raya Kasa na Sin (CDB) ya dauka game da batun samar da zunzurutun kudi har dala miliyan 254 da digo 76 (kwatankwacin dalar Amurka miliyan 254.76) domin ci gaba da aiwatar da aikin layin dogo a Nijeriya, ya kara tabbatar da gaskiyar kalaman Mr. Wang na cewa China tana daukar batutuwan da suka shafi kasashen Afirka da muhimmanci.

Shi dai wannan layin dogo mai tsawon kilomita 203, wanda zai sada biranen Kano da Kaduna, idan aka kammala shi zai taimaka wajen bunkasa harkokin zirga-zirgar jama’a, sannan kuma zai habaka harkokin tattalin arziki a yankin ta hanyar kafa masana’antu, abin da zai samar da aikin yi ga dimbin jama’a.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Abin lura a nan shi ne, zabar kasashen Afirka da ministocin harkokin wajen na kasar Sin suka saba yi a matsayin kasashen da za su fara kaiwa ziyara a cikin farkon shekara ya kara jaddada muhimmancin da kasar Sin take baiwa kawayenta kasashen Afirka. Dama dai China da Nijeriya sun dade suna cudanya da juna, suna mutunta juna kuma suna goyon bayan juna a muhimman batutuwa na kasa da kasa. Sabo da haka wannan ziyara ta Mr. Wang Yi ta kara zurfafa kyakkyawar dangantaka tsakanin kasashen biyu. (Lawal Mamuda)

Wang yi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Wang yi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Raba Kayan Makaranta Kyauta Ga Dalibai 789,000

Gwamnatin Kano Ta Raba Kayan Makaranta Kyauta Ga Dalibai 789,000

LABARAI MASU NASABA

Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

June 5, 2026
Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.