• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zulum Ya Kafa Kwamitin Bincike Game Da Gobarar Kasuwar Maiduguri

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Zulum Ya Kafa Kwamitin Bincike Game Da Gobarar Kasuwar Maiduguri
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Babagana Zulum na Jihar Borno, ya kafa wani babban kwamitin bincike mai mambobi 24 kan gobarar da ta tashi a kasuwar Monday Market a ranar Litinin a Maiduguri.

Kamfanin dillancin labarai (NAN) ya rawaito cewa wata gobara mai ban mamaki ta kone gaba daya rukunin kasuwar a ranar Lahadi.

  • Lokaci Ya Yi Da Zan Sanya Kowa Farin Ciki A Nijeriya —Tinubu
  • Da Dumi-Dumi: INEC Ta Ayyana Bola Tinubu A Matsayin Sabon Zababben Shugaban Kasa

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Usman Shuwa ya fitar a ranar Talata.

Shuwa ya ce kwamitin kuma zai dauki nauyin bayar da agajin gaggawa ga wadanda gobarar ta shafa.

Ya ce sharuddan kwamitin sun hada da tantance musabbabin aukuwar gobarar nan take, domin tantancewa da kuma tabbatar da ko akwai wasu mutane na musamman da ke da alhakin faruwar lamarin kai tsaye ko a fakaice.

Labarai Masu Nasaba

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Kwamitin a cewarsa, zai kuma duba irin girman gobarar da kuma barnar da aka yi a gine-ginen tare da tantance irin tallafin da za a bai wa wadanda gobarar ta shafa.

Haka kuma za ta tantance ainihin adadin mutanen da suka yi asara tare da tabbatar da adadin dukiyoyin da kowane daya daga cikin mutanen da suka rasa a sanadiyyar gobarar.

Kwamitin yana da Injiniya Zarami Dungus a matsayin Shugaba, yayin da Sakataren Kasuwar Monday Market zai kasance Sakataren Kwamitin.

Kamfanin Dillancin Labarai (NAN), ya ruwaito cewa, gwamnatin Jihar Borno ta fitar da Naira biliyan daya a matsayin tallafi ga wadanda abin ya shafa.

Zababben mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima da shugaban manyan makarantu (Tetfund), Kashim Ibrahim sun bayar da gudunmuwar Naira miliyan 100 kowanne.

NAN ya ruwaito cewa kasuwar ta kafu ne kimanin shekaru 35 da suka gabata yayin da kasuwar ta kasance mafi girma a yankin Arewa maso Gabas kuma jigon tattalin arzikin Borno.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GobaraKwamitiModay MarketTallafiZulum
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Inuwa Ya Yi Jimamin Rasuwar Wakilin RFI, Shehu Saulawa

Next Post

Shugaban Faransa Zai Yi Ziyarar Kwanaki 5 A Afrika

Related

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar
Labarai

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

39 minutes ago
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo
Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

2 hours ago
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

6 hours ago
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

6 hours ago
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

8 hours ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

9 hours ago
Next Post
Shugaban Faransa Zai Yi Ziyarar Kwanaki 5 A Afrika

Shugaban Faransa Zai Yi Ziyarar Kwanaki 5 A Afrika

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.