ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zulum Ya Kafa Kwamitin Bincike Game Da Gobarar Kasuwar Maiduguri

by Sadiq
4 years ago
Zulum

Gwamna Babagana Zulum na Jihar Borno, ya kafa wani babban kwamitin bincike mai mambobi 24 kan gobarar da ta tashi a kasuwar Monday Market a ranar Litinin a Maiduguri.

Kamfanin dillancin labarai (NAN) ya rawaito cewa wata gobara mai ban mamaki ta kone gaba daya rukunin kasuwar a ranar Lahadi.

  • Lokaci Ya Yi Da Zan Sanya Kowa Farin Ciki A Nijeriya —Tinubu
  • Da Dumi-Dumi: INEC Ta Ayyana Bola Tinubu A Matsayin Sabon Zababben Shugaban Kasa

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Usman Shuwa ya fitar a ranar Talata.

ADVERTISEMENT

Shuwa ya ce kwamitin kuma zai dauki nauyin bayar da agajin gaggawa ga wadanda gobarar ta shafa.

Ya ce sharuddan kwamitin sun hada da tantance musabbabin aukuwar gobarar nan take, domin tantancewa da kuma tabbatar da ko akwai wasu mutane na musamman da ke da alhakin faruwar lamarin kai tsaye ko a fakaice.

LABARAI MASU NASABA

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

Kwamitin a cewarsa, zai kuma duba irin girman gobarar da kuma barnar da aka yi a gine-ginen tare da tantance irin tallafin da za a bai wa wadanda gobarar ta shafa.

Haka kuma za ta tantance ainihin adadin mutanen da suka yi asara tare da tabbatar da adadin dukiyoyin da kowane daya daga cikin mutanen da suka rasa a sanadiyyar gobarar.

Kwamitin yana da Injiniya Zarami Dungus a matsayin Shugaba, yayin da Sakataren Kasuwar Monday Market zai kasance Sakataren Kwamitin.

Kamfanin Dillancin Labarai (NAN), ya ruwaito cewa, gwamnatin Jihar Borno ta fitar da Naira biliyan daya a matsayin tallafi ga wadanda abin ya shafa.

Zababben mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima da shugaban manyan makarantu (Tetfund), Kashim Ibrahim sun bayar da gudunmuwar Naira miliyan 100 kowanne.

NAN ya ruwaito cewa kasuwar ta kafu ne kimanin shekaru 35 da suka gabata yayin da kasuwar ta kasance mafi girma a yankin Arewa maso Gabas kuma jigon tattalin arzikin Borno.

MASU ALAKA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Next Post
Shugaban Faransa Zai Yi Ziyarar Kwanaki 5 A Afrika

Shugaban Faransa Zai Yi Ziyarar Kwanaki 5 A Afrika

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.