• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zulum Ya Raba Abinci Da Atamfa Na Miliyan 255 Ga Talakawa 70,000

by Muhammad Maitela
3 years ago
Zulum

A wani bangare na ayyukan jin kai a ziyarar kwanaki biyu a karamar hukumar Ngala, Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, a ranar Lahadi ya raba Naira miliyan 255, da kayan abinci da turamen atamfa ga maras galihu kimanin mutum 70,000.

An gudanar da raba kayayyakin ne a wurare uku: garin Ngala, Gamboru da Wulgo, dukkansu a karamar hukumar Ngala, wanda ya hada maza da mata wadanda suka ci gajiyar tallafin.

  • Bayan Kwashe Shekaru A Garkame, Zulum Ya Sake Bude Kasuwar Shanu Ta Gamboru

Tun a ranar Jummu’a Gwamna Zulum ya isa Gamboru inda ya shafe dare biyu yana gudanar da ayyukan jinkai da sauran ayyukan ci gaban yankin.

Gwamna Zulum ya ce, “Yawancin al’ummar karamar hukumar Ngala sun fuskanci ibtila’in ambaliyar ruwa wanda ya lalata gidaje da gonaki. Wanda hakan ya tilasta dole gwamnati ta sa hannu don rage tasirin matsalolin da jama’a ke fuskanta, kuma zamu ci gaba da tallafa wa mutanenmu da ke cikin bukata har sai sun samu damar tsayawa da kafafunsu.” in shi.

Kafin raba kayan abinci, tsabar kudi tare da turamen atamfa, Gwamna Zulum a ranar Asabar ya sake bude Kasuwar Shanu ta kasa da kasa ta Gamboru wadda aka rufe kusan shekaru 7 saboda ayyukan Boko Haram.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Wanda nan take manyan motocin dakon kaya na tireloli suka fara dakom dabbobi, daga kasuwar Gamboru zuwa Maiduguri da sauran sassan Nijeriya.

Gwamna Zulum ya bayyana godiyarsa ga shugaban kasa Muhammadu Buhari bisa gagarumin kokari tare da shugabanci nagari, wanda ya haifar da zaman lafiya a Borno da fadin kasar nan baki daya.

A hannu guda kuma, Gwamna Zulum ya yaba wa sojojin Nijeriya hadi da sauran jami’an tsaro bisa sadaukarwar da suka nuna wajen samar da yanayi mai kyau da ya ba da damar maido da harkokin tattalin arziki a fadin jihar Borno.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 
Manyan Labarai

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya
Labarai

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Next Post
An Jinjinawa Matakan Sin Na Shawo Kan Kalubalen Sauyin Yanayi

An Jinjinawa Matakan Sin Na Shawo Kan Kalubalen Sauyin Yanayi

LABARAI MASU NASABA

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.