Faeza Mustapha">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home DAGA BIRNIN SIN

Zumunta A Kafa Take

by Faeza Mustapha
January 5, 2021
in DAGA BIRNIN SIN
2 min read
Zumunta A Kafa Take
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Tun daga jiya Litinin, 4 ga watan nan na Junairu, mamban majalisar gudanarwar kasar Sin, kuma ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya fara ziyartar wasu kasashe 5 na nahiyar Afrika, da suka hada da Najeriya, da Congo (Kinshasa), da Botswana, da Tanzania, da Seychelles, ziyarar da zai kammala a ranar 9 ga wata. Ziyarar ministan harkokin wajen kasar Sin a kasashen Afrika a farkon kowacce shekara, ta zama wata kyakkyawar al’adar da ake ta daukaka ta tun daga shekarar 1991, wato shekaru 30 cif da suka gabata.

Kamar yadda ake cewa aminci da dangantakar Sin da Afrika daddadiya ce, tabbas wannan al’ada da ake ci gaba da rayawa, daya ce daga cikin shaidun dake tabbatar da hakan. Duk da yanayin da duniya ta tsinci kanta na fama da annobar COVID-19 mai yaduwa kamar wutar daji, Sin ba ta yi kasa a gwiwa ba wajen ci gaba da wannan al’ada, tabbas wannan ya nuna abun da ake cewa, aboki na kwarai shi ne mai kasancewa da kai komai wuya komai rintsi.
Ziyarar ta Wang Yi a bana, ta zo a shekarar da za a kammala aiwatar da batutuwan da aka cimma yayin taron kolin Beijing, na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afrika wato FOCAC da aka tsara aiwatarwa tsakanin shekarar 2019 zuwa 2021. Ya kamata a ce wannan ziyara, ta share fagen tsara karin ayyuka, ko dorawa kan nasarorin da aka samu kan hadin gwiwar, wadanda suka shafi inganta dangantakarsu a fannonin cinikayya da samar da kayayyakin more rayuwa da musaya da kiwon lafiya da sauransu. Idan za a yi misali da ginin ababen more rayuwa da kasar Sin ke aiwatarwa a nahiyar Afrika, za a iya cewa ya dora nahiyar kan tafarkin samun ci gaba. A wannan gaba da aka fara amfani da yarjejeniyar yankin ciniki cikin ’yanci tsakanin kasashen nahiyar Afrika, hadin gwiwarsu da kasar Sin zai taka rawa matuka, a matsayinta na wadda ta ci gaba kuma mai gogewa. Gogewar kasar Sin zai zamarwa kasashen abun koyi da dogaro a fannin raya masana’antu da kuma samar da ababen more rayuwa da za su saukaka harkokin cinikayya da hade kasashen nahiyar kamar yadda suke fata.
Akwai kuma batun yaki da annobar COVID-19 da farfado da tattalin arziki daga halin da ya shiga sanadiyyar tasirin annobar. Abun nufi shi ne, zai yi kyau idan kasashen za su yi amfani da wannan dama ta ziyarar ministan harkokin wajen kasar Sin, su kara zurfafa hadin gwiwa da kasar, don ganowa tare da koyo dabarunta na yaki da cutar, ganin irin nasarar da ta samu a bangaren kawo yanzu. Sannan duk da tasirin annobar kan tattalin arzikin daukacin kasashen duniya, ta yi namijin kokari wajen zama kasa daya tilo da ta samu ci gaban tattalin arziki a bara. Don haka, hadin gwiwa da kasar Sin abu ne da ya zama wajibi domin ta kasance abar koyi kuma mai kaifin basira.
Ya kamata wannan ziyara ta kara tunatarwa kasashen Afrika da ma yammacin duniya cewa, Sin da gaske take dangane da zumunci da furuci da burinta na tallafawa kasashen Afrika. Duk da yadda harkokin rayuwa suka sauya a duniya a baya-bayan nan, Sin ta dage wajen daukaka zumuncin dake tsakaninta da ’yan uwanta na nahiyar Afrika, ta ci gaba da daukaka al’adarta da nufin karfafa dangantaka, lamarin da ya kuma haska yadda take daukar nahiyar Afrikar da al’ummominta da batutuwan da suka shafe ta da muhimmanci. (Faeza Mustapha)

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Masanan Sin Sun Karyata Zargin Kasashen Yamma Kan Batun Al’ummar Xinjiang

Next Post

Saura Kiris A Rabu Da Matsin Tattalin Arziki A Nijeriya — Gwamnatin Tarayya

RelatedPosts

Sanya Takunkumi Kan Pompeo Da Sauran Wasu Amurkawa 27 Abu Ne Da Ya Dace

Sanya Takunkumi Kan Pompeo Da Sauran Wasu Amurkawa 27 Abu Ne Da Ya Dace

by Faeza Mustapha
3 hours ago
0

Kwanan nan, gwamnatin kasar Sin ta sanar da sanya takunkumi...

Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Ketare A Shekarar 2020 Ya Karu Da 3.3%

Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Ketare A Shekarar 2020 Ya Karu Da 3.3%

by Faeza Mustapha
4 hours ago
0

Kididdigar da ma’aikatar kasuwanci ta kasar Sin da hukumar kula...

Xi Ya Jaddada Muhimmancin Aiki Da Dokokin Jam’iyya A Lokacin Aiwatar Da Ajandar Raya Kasa Ta Shekaru 5 Karo Na 14

Xi Ya Jaddada Muhimmancin Aiki Da Dokokin Jam’iyya A Lokacin Aiwatar Da Ajandar Raya Kasa Ta Shekaru 5 Karo Na 14

by Faeza Mustapha
4 hours ago
0

Shugaban kasar Sin, kuma babban sakataren kwamitin kolin JKS Xi...

Next Post
Saura Kiris A Rabu Da Matsin Tattalin Arziki A Nijeriya — Gwamnatin Tarayya

Saura Kiris A Rabu Da Matsin Tattalin Arziki A Nijeriya — Gwamnatin Tarayya

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version