Ministan ma’adinai da karafa, Arc. Olamilekan Adegbite, ya bayyana cewa dimbin albarkatun ma’adinai dake baje a ko’ina cikin kasar Nijeriya na da damar sanya kasar zama “mafi kyawun wurin saka hannun jari a duniya, wanda hakan zai sauya tattalin arzikin kasar.”
Ministan ya bayyana hakan ne a hedikwatar ma’aikatar da ke Abuja gabanin taron makon Ma’adinan Nijeriya na shekarar 2022 da ake shirye-shiryen gudanarwa nan gaba kadan Yayin tattaunawa da manema labarai.
Adegbite ya bayyana cewa, taron makon ma’adinan Nijeriya da aka shirya gudanarwa tsakanin ranakun 1 zuwa 3 ga watan Nuwamba, 2022, a cibiyar taro ta kasa da kasa dake Abuja, wani bangare ne da ma’aikatar ta ke yi na nunawa duniya cewa, Nijeriya cike take da Ma’adanai kuma sashen ma’adinan a shirye yake don amsar masu zuba Jari.
Ministan ya kuma bayyana cewa, muhimman batutuwan da za a tattauna a taron za su hada da muhimman albarkatun ma’adinai wadanda su ne tubalin gina fasahohi wadanda da dama da su ake amfani wajen samarwa duniya makamashin zamani mai karancin cutarwa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp