• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙungiyar Dambe Warriors Ta Gayyato Ɗan Damben Saudiyya Don Fafata Wasan Ƙarshe A Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
2 years ago
in Labarai
0
Ƙungiyar Dambe Warriors Ta Gayyato Ɗan Damben Saudiyya Don Fafata Wasan Ƙarshe A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ƙungiyar masu wasan dambe ta “Dambe Warriors” ta ƙudiri aniyar ganin an sake fasalin harkar dambe zuwa ta zamani don sana’ar ta zama mai kawo rufin asiri mai yawa.

Shugaban kungiyar, Alhaji Aminu Bature ne ya bayyana haka a lokacin taron manema labarai da kungiyar ta gudanar a Otal ɗin CACID dake Kano domin bayyana wa duniya irin kyakkyawan shirin da suka yi don gudanar da wasan dambe a Kano cikin mako mai zuwa a filin wasa na Kano Pillars da ke Sabon Gari.

Shugaban ya bayanna cewa a baya ‘yan Dambe suna yi ne kawai a matsayin al’adar Hausa, amma ba don samun wani rufin asiri ba.

“Saboda haka yace yanzu tun da Allah ya sa muka kafa wannan kungiyar kowa ya ga irin nasarar da aka samu, wanda yanzu haka mun je jihohi da yawa na kasar nan da ma makwabta.

dambe
Ɗaya daga cikin jaruman da za a fafata da su, Dogo Sissco

“Na shafe sama da shekara 20 ina yayin dambe, saboda haka na san farin sa da bakinsa, wannan ta sa aka zabe ni a matsayin shugaban kungiyar Dambe Warriors kuma muka tsara sake fasalin Dambe domin tafiya daidai da zamani, sannan kuma a baya dan dambe dan abinda yake samu bai taka kara ya karya ba.

Labarai Masu Nasaba

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

“Yanzu haka muna da rukunin ‘yan damben da suke daukar albashin Naira dubu 370,000.00 ga matsakaita girma da kuma masu ɗaukar Naira 570,000.00 duk wata, sannan kuma wasan damben da ake shirin gudanar da zagaye na karshe a Kano nan ba da jimawa ba duk wanda ya samu Nasara zai yi hafzi da Naira Miliyan guda yayin da sauran za su samu Naira dubu 500,000.

“Sannan kuma a wannan karon za a gudanar da wasan zagayen ƙarshe tare da guda cikin ‘yan damben kasar Saudiyya wanda tuni ya iso muna gudanar da tsare-tsaren da suka rage.” In ji shi.

  • Zargin Kafar Angulu Ga Dimokuradiyyar Nijeriya: Cacar Baki Ta Barke Tsakanin ‘Yan Adawa Da Gwamnati

A karshe shugaban ya jinjina wa abokan aikinsa na dambe tare da yaba wa mai martaba Sarkin Kano wanda shi da kansa ya bayar da kofin da ake sa ran lashewa a lokacin wasan karshe.

Cikin ‘yawan ‘yan damben da za su fafata sun hada da Autan Ali Kanen Bello, Bahago Zayyanu, Dogo Sissco, Hussein ɗan Ƙasar Saudiyya da Sauran ‘yan wasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BoxingDambekanoNigeriaSaudi ArabiaSaudiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 7 Da Cafke 33 A Kaduna Da Filato

Next Post

Da Ɗumi-ɗuminsa: ‘Yan Bindiga Sun Sace Fiye Da Mutum 150 A Zamfara

Related

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Labarai

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

7 hours ago
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi
Labarai

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

8 hours ago
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa
Labarai

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

8 hours ago
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

9 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

11 hours ago
Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 
Labarai

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

12 hours ago
Next Post
Da Ɗumi-ɗuminsa: ‘Yan Bindiga Sun Sace Fiye Da Mutum 150 A Zamfara

Da Ɗumi-ɗuminsa: 'Yan Bindiga Sun Sace Fiye Da Mutum 150 A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.