• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙungiyar Dambe Warriors Ta Gayyato Ɗan Damben Saudiyya Don Fafata Wasan Ƙarshe A Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
2 years ago
dambe

Ƙungiyar masu wasan dambe ta “Dambe Warriors” ta ƙudiri aniyar ganin an sake fasalin harkar dambe zuwa ta zamani don sana’ar ta zama mai kawo rufin asiri mai yawa.

Shugaban kungiyar, Alhaji Aminu Bature ne ya bayyana haka a lokacin taron manema labarai da kungiyar ta gudanar a Otal ɗin CACID dake Kano domin bayyana wa duniya irin kyakkyawan shirin da suka yi don gudanar da wasan dambe a Kano cikin mako mai zuwa a filin wasa na Kano Pillars da ke Sabon Gari.

Shugaban ya bayanna cewa a baya ‘yan Dambe suna yi ne kawai a matsayin al’adar Hausa, amma ba don samun wani rufin asiri ba.

“Saboda haka yace yanzu tun da Allah ya sa muka kafa wannan kungiyar kowa ya ga irin nasarar da aka samu, wanda yanzu haka mun je jihohi da yawa na kasar nan da ma makwabta.

dambe
Ɗaya daga cikin jaruman da za a fafata da su, Dogo Sissco

“Na shafe sama da shekara 20 ina yayin dambe, saboda haka na san farin sa da bakinsa, wannan ta sa aka zabe ni a matsayin shugaban kungiyar Dambe Warriors kuma muka tsara sake fasalin Dambe domin tafiya daidai da zamani, sannan kuma a baya dan dambe dan abinda yake samu bai taka kara ya karya ba.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

“Yanzu haka muna da rukunin ‘yan damben da suke daukar albashin Naira dubu 370,000.00 ga matsakaita girma da kuma masu ɗaukar Naira 570,000.00 duk wata, sannan kuma wasan damben da ake shirin gudanar da zagaye na karshe a Kano nan ba da jimawa ba duk wanda ya samu Nasara zai yi hafzi da Naira Miliyan guda yayin da sauran za su samu Naira dubu 500,000.

“Sannan kuma a wannan karon za a gudanar da wasan zagayen ƙarshe tare da guda cikin ‘yan damben kasar Saudiyya wanda tuni ya iso muna gudanar da tsare-tsaren da suka rage.” In ji shi.

  • Zargin Kafar Angulu Ga Dimokuradiyyar Nijeriya: Cacar Baki Ta Barke Tsakanin ‘Yan Adawa Da Gwamnati

A karshe shugaban ya jinjina wa abokan aikinsa na dambe tare da yaba wa mai martaba Sarkin Kano wanda shi da kansa ya bayar da kofin da ake sa ran lashewa a lokacin wasan karshe.

Cikin ‘yawan ‘yan damben da za su fafata sun hada da Autan Ali Kanen Bello, Bahago Zayyanu, Dogo Sissco, Hussein ɗan Ƙasar Saudiyya da Sauran ‘yan wasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima
Manyan Labarai

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Next Post
Da Ɗumi-ɗuminsa: ‘Yan Bindiga Sun Sace Fiye Da Mutum 150 A Zamfara

Da Ɗumi-ɗuminsa: 'Yan Bindiga Sun Sace Fiye Da Mutum 150 A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.