ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗalibi A Fannin Karatun Lauya Ya Kashe Kansa A Adamawa

by Rabi'u Ali Indabawa
7 days ago
Kashe

An ruwaito cewa wani dalibin Makarantar Lauyoyi ta Nijeriya Ayomiposi Ojajuni, ya kashe kansa bayan an hana shi rubuta jarabawar karshe ta Bar Final a sansanin Yola, Jihar Adamawa.

PUNCH Metro ta samu labarin daga akalla dalibai biyu da suka san lamarin, wadanda suka yi magana karkashin sharadi na boye sunansu saboda yadda al’amarin ya ke da sarkakiya, cewa lamarin ya faru ne a ranar Asabar.

An ce Ojajuni, wanda ya kammala karatunsa a Olabisi Onabanjo Unibersity, an yi masa jerin tambayoyi daga shugabannin makarantar, daga bisani kuma aka gano cewa ba za a ba shi damar halartar jarabawar kwararru ba, wadda ta fara a ranar daya.

ADVERTISEMENT

Wani dalibi a makarantar lauya da ya yi magana da wakilinmu a ranar Lahadi cewa, “An yi masa tambayoyi a baya. Ko da ba mu san cikakken abin tambayoyin ba, daga baya ya gano cewa ba za a ba shi damar shiga jarabawar ba. Wannan ne ya sa ya shiga damuwa sosai, kuma hakan ne ya jawo mutuwarsa.”

Wani dalibi a makarantar ya ce Ojajuni ya rasu ne bayan shan wata guba.

LABARAI MASU NASABA

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

“Ya sha wani abu mai hadari a ranar Asabar kuma ya rasu a ranar Lahadi bayan an kai shi Asibitin Koyarwa na Jami’ar Modibbo Adama, Yola,” in ji shi.

Lokacin da aka tuntubi mai magana da yawun Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Adamawa, Yahaya Suleiman, a ranar Lahadi, ya ce, “Ba a ba ni izinin yin sharhi kan wani aikin jarabawa na hukuma ba. Ina Abuja.

Na dai karanta labarin ne a jarida kamar yadda ku kuka karanta.”

A halin da ake ciki, wata kafar labarai ta Intanet, FactCheckNews, ta ruwaito a ranar Lahadi cewa Ojajuni ya kashe kansa ne bayan kasa cika kashi 75 cikin 100 na halartar darussa da ake bukata domin cancantar shiga jarabawa.

“Majiyoyi a sansanin makarantar sun shaida wa wakilinmu cewa a baya, sunan wadanda suka cancanci shiga jarabawa kan fito makonni biyu kafin jarabawar, wanda hakan ke ba wa dalibai da ba su kai kashi 75 cikin 100 ba bisa dalilan lafiya na gaskiya damar gyara matsalarsu.

“Amma a kwanan nan, makarantar ta dauki sabon tsari na sanya sunayen ne a karshe kafin jarabawa, ba tare da barin wani lokaci don gyara irin wadannan halaye ba.”

  • NDLEA Ta Kama Kilo 588 Na Miyagun Ƙwayoyi, Ta Ƙona Hekta 6 Na Gonakin Wiwi A Adamawa
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Uku Bayan Rufe Makarantu A Adamawa

“Bayan ganin cewa bai cancanci shiga jarabawar ba, dalibin ya sha wani abu da ake kyautata zaton gubar bera ce, wanda hakan ya jawo masa rashin lafiya mai tsanani har ya rasu,” in ji kafar labaran.

Lokacin da aka tuntubi Jami’in Hulda da Jama’a na ‘Yan Sanda na Jihar, Suleiman Nguroje, ya ce har yanzu ba a kai rahoton lamarin gare su ba.

Ya ce, “Har yanzu ba mu sami irin wannan rahoton ba. Na kira DPO a yankin, amma ya ce bai samu rahoton ba. Haka nan na yi kokarin kiran makarantar lauya, amma ban samu nasarar samun su ba.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli
Labarai

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Next Post
Kamfanin Hakar Danyen Mai A Teku Na Sin Ya Sanar Da Fara Aiki A Mataki Na Biyu Na Hakar Mai A Yankin Teku Mai Zurfi

Kamfanin Hakar Danyen Mai A Teku Na Sin Ya Sanar Da Fara Aiki A Mataki Na Biyu Na Hakar Mai A Yankin Teku Mai Zurfi

LABARAI MASU NASABA

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.