ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗalibi A Fannin Karatun Lauya Ya Kashe Kansa A Adamawa

by Rabi'u Ali Indabawa
9 months ago
Kashe

An ruwaito cewa wani dalibin Makarantar Lauyoyi ta Nijeriya Ayomiposi Ojajuni, ya kashe kansa bayan an hana shi rubuta jarabawar karshe ta Bar Final a sansanin Yola, Jihar Adamawa.

PUNCH Metro ta samu labarin daga akalla dalibai biyu da suka san lamarin, wadanda suka yi magana karkashin sharadi na boye sunansu saboda yadda al’amarin ya ke da sarkakiya, cewa lamarin ya faru ne a ranar Asabar.

An ce Ojajuni, wanda ya kammala karatunsa a Olabisi Onabanjo Unibersity, an yi masa jerin tambayoyi daga shugabannin makarantar, daga bisani kuma aka gano cewa ba za a ba shi damar halartar jarabawar kwararru ba, wadda ta fara a ranar daya.

ADVERTISEMENT

Wani dalibi a makarantar lauya da ya yi magana da wakilinmu a ranar Lahadi cewa, “An yi masa tambayoyi a baya. Ko da ba mu san cikakken abin tambayoyin ba, daga baya ya gano cewa ba za a ba shi damar shiga jarabawar ba. Wannan ne ya sa ya shiga damuwa sosai, kuma hakan ne ya jawo mutuwarsa.”

Wani dalibi a makarantar ya ce Ojajuni ya rasu ne bayan shan wata guba.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

“Ya sha wani abu mai hadari a ranar Asabar kuma ya rasu a ranar Lahadi bayan an kai shi Asibitin Koyarwa na Jami’ar Modibbo Adama, Yola,” in ji shi.

Lokacin da aka tuntubi mai magana da yawun Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Adamawa, Yahaya Suleiman, a ranar Lahadi, ya ce, “Ba a ba ni izinin yin sharhi kan wani aikin jarabawa na hukuma ba. Ina Abuja.

Na dai karanta labarin ne a jarida kamar yadda ku kuka karanta.”

A halin da ake ciki, wata kafar labarai ta Intanet, FactCheckNews, ta ruwaito a ranar Lahadi cewa Ojajuni ya kashe kansa ne bayan kasa cika kashi 75 cikin 100 na halartar darussa da ake bukata domin cancantar shiga jarabawa.

“Majiyoyi a sansanin makarantar sun shaida wa wakilinmu cewa a baya, sunan wadanda suka cancanci shiga jarabawa kan fito makonni biyu kafin jarabawar, wanda hakan ke ba wa dalibai da ba su kai kashi 75 cikin 100 ba bisa dalilan lafiya na gaskiya damar gyara matsalarsu.

“Amma a kwanan nan, makarantar ta dauki sabon tsari na sanya sunayen ne a karshe kafin jarabawa, ba tare da barin wani lokaci don gyara irin wadannan halaye ba.”

  • NDLEA Ta Kama Kilo 588 Na Miyagun Ƙwayoyi, Ta Ƙona Hekta 6 Na Gonakin Wiwi A Adamawa
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Uku Bayan Rufe Makarantu A Adamawa

“Bayan ganin cewa bai cancanci shiga jarabawar ba, dalibin ya sha wani abu da ake kyautata zaton gubar bera ce, wanda hakan ya jawo masa rashin lafiya mai tsanani har ya rasu,” in ji kafar labaran.

Lokacin da aka tuntubi Jami’in Hulda da Jama’a na ‘Yan Sanda na Jihar, Suleiman Nguroje, ya ce har yanzu ba a kai rahoton lamarin gare su ba.

Ya ce, “Har yanzu ba mu sami irin wannan rahoton ba. Na kira DPO a yankin, amma ya ce bai samu rahoton ba. Haka nan na yi kokarin kiran makarantar lauya, amma ban samu nasarar samun su ba.”

Kashe
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Kamfanin Hakar Danyen Mai A Teku Na Sin Ya Sanar Da Fara Aiki A Mataki Na Biyu Na Hakar Mai A Yankin Teku Mai Zurfi

Kamfanin Hakar Danyen Mai A Teku Na Sin Ya Sanar Da Fara Aiki A Mataki Na Biyu Na Hakar Mai A Yankin Teku Mai Zurfi

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.