ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗalibi A Fannin Karatun Lauya Ya Kashe Kansa A Adamawa

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
Kashe

An ruwaito cewa wani dalibin Makarantar Lauyoyi ta Nijeriya Ayomiposi Ojajuni, ya kashe kansa bayan an hana shi rubuta jarabawar karshe ta Bar Final a sansanin Yola, Jihar Adamawa.

PUNCH Metro ta samu labarin daga akalla dalibai biyu da suka san lamarin, wadanda suka yi magana karkashin sharadi na boye sunansu saboda yadda al’amarin ya ke da sarkakiya, cewa lamarin ya faru ne a ranar Asabar.

An ce Ojajuni, wanda ya kammala karatunsa a Olabisi Onabanjo Unibersity, an yi masa jerin tambayoyi daga shugabannin makarantar, daga bisani kuma aka gano cewa ba za a ba shi damar halartar jarabawar kwararru ba, wadda ta fara a ranar daya.

ADVERTISEMENT

Wani dalibi a makarantar lauya da ya yi magana da wakilinmu a ranar Lahadi cewa, “An yi masa tambayoyi a baya. Ko da ba mu san cikakken abin tambayoyin ba, daga baya ya gano cewa ba za a ba shi damar shiga jarabawar ba. Wannan ne ya sa ya shiga damuwa sosai, kuma hakan ne ya jawo mutuwarsa.”

Wani dalibi a makarantar ya ce Ojajuni ya rasu ne bayan shan wata guba.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

“Ya sha wani abu mai hadari a ranar Asabar kuma ya rasu a ranar Lahadi bayan an kai shi Asibitin Koyarwa na Jami’ar Modibbo Adama, Yola,” in ji shi.

Lokacin da aka tuntubi mai magana da yawun Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Adamawa, Yahaya Suleiman, a ranar Lahadi, ya ce, “Ba a ba ni izinin yin sharhi kan wani aikin jarabawa na hukuma ba. Ina Abuja.

Na dai karanta labarin ne a jarida kamar yadda ku kuka karanta.”

A halin da ake ciki, wata kafar labarai ta Intanet, FactCheckNews, ta ruwaito a ranar Lahadi cewa Ojajuni ya kashe kansa ne bayan kasa cika kashi 75 cikin 100 na halartar darussa da ake bukata domin cancantar shiga jarabawa.

“Majiyoyi a sansanin makarantar sun shaida wa wakilinmu cewa a baya, sunan wadanda suka cancanci shiga jarabawa kan fito makonni biyu kafin jarabawar, wanda hakan ke ba wa dalibai da ba su kai kashi 75 cikin 100 ba bisa dalilan lafiya na gaskiya damar gyara matsalarsu.

“Amma a kwanan nan, makarantar ta dauki sabon tsari na sanya sunayen ne a karshe kafin jarabawa, ba tare da barin wani lokaci don gyara irin wadannan halaye ba.”

  • NDLEA Ta Kama Kilo 588 Na Miyagun Ƙwayoyi, Ta Ƙona Hekta 6 Na Gonakin Wiwi A Adamawa
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Uku Bayan Rufe Makarantu A Adamawa

“Bayan ganin cewa bai cancanci shiga jarabawar ba, dalibin ya sha wani abu da ake kyautata zaton gubar bera ce, wanda hakan ya jawo masa rashin lafiya mai tsanani har ya rasu,” in ji kafar labaran.

Lokacin da aka tuntubi Jami’in Hulda da Jama’a na ‘Yan Sanda na Jihar, Suleiman Nguroje, ya ce har yanzu ba a kai rahoton lamarin gare su ba.

Ya ce, “Har yanzu ba mu sami irin wannan rahoton ba. Na kira DPO a yankin, amma ya ce bai samu rahoton ba. Haka nan na yi kokarin kiran makarantar lauya, amma ban samu nasarar samun su ba.”

Kashe
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Kamfanin Hakar Danyen Mai A Teku Na Sin Ya Sanar Da Fara Aiki A Mataki Na Biyu Na Hakar Mai A Yankin Teku Mai Zurfi

Kamfanin Hakar Danyen Mai A Teku Na Sin Ya Sanar Da Fara Aiki A Mataki Na Biyu Na Hakar Mai A Yankin Teku Mai Zurfi

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.