ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗalibi A Fannin Karatun Lauya Ya Kashe Kansa A Adamawa

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
Kashe

An ruwaito cewa wani dalibin Makarantar Lauyoyi ta Nijeriya Ayomiposi Ojajuni, ya kashe kansa bayan an hana shi rubuta jarabawar karshe ta Bar Final a sansanin Yola, Jihar Adamawa.

PUNCH Metro ta samu labarin daga akalla dalibai biyu da suka san lamarin, wadanda suka yi magana karkashin sharadi na boye sunansu saboda yadda al’amarin ya ke da sarkakiya, cewa lamarin ya faru ne a ranar Asabar.

An ce Ojajuni, wanda ya kammala karatunsa a Olabisi Onabanjo Unibersity, an yi masa jerin tambayoyi daga shugabannin makarantar, daga bisani kuma aka gano cewa ba za a ba shi damar halartar jarabawar kwararru ba, wadda ta fara a ranar daya.

ADVERTISEMENT

Wani dalibi a makarantar lauya da ya yi magana da wakilinmu a ranar Lahadi cewa, “An yi masa tambayoyi a baya. Ko da ba mu san cikakken abin tambayoyin ba, daga baya ya gano cewa ba za a ba shi damar shiga jarabawar ba. Wannan ne ya sa ya shiga damuwa sosai, kuma hakan ne ya jawo mutuwarsa.”

Wani dalibi a makarantar ya ce Ojajuni ya rasu ne bayan shan wata guba.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

“Ya sha wani abu mai hadari a ranar Asabar kuma ya rasu a ranar Lahadi bayan an kai shi Asibitin Koyarwa na Jami’ar Modibbo Adama, Yola,” in ji shi.

Lokacin da aka tuntubi mai magana da yawun Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Adamawa, Yahaya Suleiman, a ranar Lahadi, ya ce, “Ba a ba ni izinin yin sharhi kan wani aikin jarabawa na hukuma ba. Ina Abuja.

Na dai karanta labarin ne a jarida kamar yadda ku kuka karanta.”

A halin da ake ciki, wata kafar labarai ta Intanet, FactCheckNews, ta ruwaito a ranar Lahadi cewa Ojajuni ya kashe kansa ne bayan kasa cika kashi 75 cikin 100 na halartar darussa da ake bukata domin cancantar shiga jarabawa.

“Majiyoyi a sansanin makarantar sun shaida wa wakilinmu cewa a baya, sunan wadanda suka cancanci shiga jarabawa kan fito makonni biyu kafin jarabawar, wanda hakan ke ba wa dalibai da ba su kai kashi 75 cikin 100 ba bisa dalilan lafiya na gaskiya damar gyara matsalarsu.

“Amma a kwanan nan, makarantar ta dauki sabon tsari na sanya sunayen ne a karshe kafin jarabawa, ba tare da barin wani lokaci don gyara irin wadannan halaye ba.”

  • NDLEA Ta Kama Kilo 588 Na Miyagun Ƙwayoyi, Ta Ƙona Hekta 6 Na Gonakin Wiwi A Adamawa
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Uku Bayan Rufe Makarantu A Adamawa

“Bayan ganin cewa bai cancanci shiga jarabawar ba, dalibin ya sha wani abu da ake kyautata zaton gubar bera ce, wanda hakan ya jawo masa rashin lafiya mai tsanani har ya rasu,” in ji kafar labaran.

Lokacin da aka tuntubi Jami’in Hulda da Jama’a na ‘Yan Sanda na Jihar, Suleiman Nguroje, ya ce har yanzu ba a kai rahoton lamarin gare su ba.

Ya ce, “Har yanzu ba mu sami irin wannan rahoton ba. Na kira DPO a yankin, amma ya ce bai samu rahoton ba. Haka nan na yi kokarin kiran makarantar lauya, amma ban samu nasarar samun su ba.”

Kashe
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Next Post
Kamfanin Hakar Danyen Mai A Teku Na Sin Ya Sanar Da Fara Aiki A Mataki Na Biyu Na Hakar Mai A Yankin Teku Mai Zurfi

Kamfanin Hakar Danyen Mai A Teku Na Sin Ya Sanar Da Fara Aiki A Mataki Na Biyu Na Hakar Mai A Yankin Teku Mai Zurfi

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.