ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“Ɗaukar Abdulkarim Daura Matsayin Mataimakin Gwamna Zai Kawo Wa APC Nasara A Katsina”

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
APC

An yi kira ga masu ruwa da tsaki a jam’iyyar APC na jihar Katsina da su yi karatun ta nutsu su sake tunani game da ɗaukar ɗan takarar mataimakin gwamnan jihar Katsina a zaɓen 2023 mai zuwa.

Wani matashi ɗan jami’yyar APC a garin Katsina Sule Dudu Kofar Marusa ya yi wannan kiran a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Katsina.

  • Mutane 6 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Ondo

 

ADVERTISEMENT

Abdulkarim Dauda Daura na ɗaya daga cikin mutane tara da suka shiga zaɓen fidda gwani amma bai samu nasara ba a ƙarƙashin jam’iyar APC a jihar Katsina.

Sule Dudu Kofar Marusa ya ce idan jami’yyar APC ya ɗauki Abdulkarim Dauda Daura a matsayin wanda zai yi wa ɗan takarar jam’iyyar APC mataimaki zai taimaka wajan shawo kan matsalar tsaro.

LABARAI MASU NASABA

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

Ya kuma ƙara da cewa har yanzu wuri bai korewa jami’yyar APC ba kasancewar Abdulkarim Dauda Daura masanin tsaro ne duba da irin yanayin da jihar Katsina ta shiga akan halin rashin tsaro.

“Abdulkarim Dauda Daura masanin tsaro ne, wanda yanzu haka yana ƙasashen waje akan abinda ya shafi sha’anin tsaro a duniya, inda ya ziyarci Kasashen Mexico da France da Italy da sauran su” inji shi.

Matashin dai ya ƙara da cewa idan har Masari da Dikko Umar Raɗɗa da Jami’yyar APC suna son cin zaɓe to su jawo A.D Daura su bashi mataimaki gwamna domin samun nasara a zaɓen 2023.

Haka kuma Sule Dudu ya yi bayanin cewa A.D Daura yana da kyakkyawan tarihi a lokacin da ya yi aikin ɗan Sanda, ba a taɓa kama shi da cin amana ba, sannan ya samawa jama’a da dama aikin yi fiye da mutane dubu biyar (5,000)

Sule Dudu ya ce idan jami’yyar APC ta ɗauki Abdulkarim Dauda Daura mataimakin gwamna za su samu mafita kuma wuri bai kore ba, yana mai cewa hakan zai baiwa yankin Daura mai ƙananan hukumomi 12 kawo kuri’unsu fiye da kashi 75%

“Lallai ya kamata jami’yyar mu ta APC ta san cewa Annabi ya fako, ta sake tunani, ta yi abinda ya kamata, duba da cewa akwai wasu alƙawura da har yanzu bata cika ba, wanda idan ba a yi abinda ya kamata ba, za a yi samun matsala” inji Sule Dudu

Daga karshe ya yi kira ga jama’a da su ajiye siyasa gefe guda akan matsalar tsaro, saboda shi dai ɗan ta’adda baya da gwani kowa ɗauka yake, ba ruwan shi da ɗan APC ko ɗan PDP koma wace irin jami’yya kamawa yake.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP
Siyasa

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

November 12, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
Siyasa

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Next Post
Wani Ya Yi Alkawarin Auren Matashiyar Da Aka Yi Wa Sanadin Rasa Kafa A Sakkwato

Wani Ya Yi Alkawarin Auren Matashiyar Da Aka Yi Wa Sanadin Rasa Kafa A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.