• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“Ɗaukar Abdulkarim Daura Matsayin Mataimakin Gwamna Zai Kawo Wa APC Nasara A Katsina”

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
in Siyasa
0
“Ɗaukar Abdulkarim Daura Matsayin Mataimakin Gwamna Zai Kawo Wa APC Nasara A Katsina”
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An yi kira ga masu ruwa da tsaki a jam’iyyar APC na jihar Katsina da su yi karatun ta nutsu su sake tunani game da ɗaukar ɗan takarar mataimakin gwamnan jihar Katsina a zaɓen 2023 mai zuwa.

Wani matashi ɗan jami’yyar APC a garin Katsina Sule Dudu Kofar Marusa ya yi wannan kiran a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Katsina.

  • Mutane 6 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Ondo

 

Abdulkarim Dauda Daura na ɗaya daga cikin mutane tara da suka shiga zaɓen fidda gwani amma bai samu nasara ba a ƙarƙashin jam’iyar APC a jihar Katsina.

Sule Dudu Kofar Marusa ya ce idan jami’yyar APC ya ɗauki Abdulkarim Dauda Daura a matsayin wanda zai yi wa ɗan takarar jam’iyyar APC mataimaki zai taimaka wajan shawo kan matsalar tsaro.

Labarai Masu Nasaba

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

Ya kuma ƙara da cewa har yanzu wuri bai korewa jami’yyar APC ba kasancewar Abdulkarim Dauda Daura masanin tsaro ne duba da irin yanayin da jihar Katsina ta shiga akan halin rashin tsaro.

“Abdulkarim Dauda Daura masanin tsaro ne, wanda yanzu haka yana ƙasashen waje akan abinda ya shafi sha’anin tsaro a duniya, inda ya ziyarci Kasashen Mexico da France da Italy da sauran su” inji shi.

Matashin dai ya ƙara da cewa idan har Masari da Dikko Umar Raɗɗa da Jami’yyar APC suna son cin zaɓe to su jawo A.D Daura su bashi mataimaki gwamna domin samun nasara a zaɓen 2023.

Haka kuma Sule Dudu ya yi bayanin cewa A.D Daura yana da kyakkyawan tarihi a lokacin da ya yi aikin ɗan Sanda, ba a taɓa kama shi da cin amana ba, sannan ya samawa jama’a da dama aikin yi fiye da mutane dubu biyar (5,000)

Sule Dudu ya ce idan jami’yyar APC ta ɗauki Abdulkarim Dauda Daura mataimakin gwamna za su samu mafita kuma wuri bai kore ba, yana mai cewa hakan zai baiwa yankin Daura mai ƙananan hukumomi 12 kawo kuri’unsu fiye da kashi 75%

“Lallai ya kamata jami’yyar mu ta APC ta san cewa Annabi ya fako, ta sake tunani, ta yi abinda ya kamata, duba da cewa akwai wasu alƙawura da har yanzu bata cika ba, wanda idan ba a yi abinda ya kamata ba, za a yi samun matsala” inji Sule Dudu

Daga karshe ya yi kira ga jama’a da su ajiye siyasa gefe guda akan matsalar tsaro, saboda shi dai ɗan ta’adda baya da gwani kowa ɗauka yake, ba ruwan shi da ɗan APC ko ɗan PDP koma wace irin jami’yya kamawa yake.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin: Ya Kamata A Girmama Ikon Mulkin Kasa Da Cikakkun Yankunan Kasa Yayin Da Kasashen Duniya Suke Mu’amala Da Juna

Next Post

Wani Ya Yi Alkawarin Auren Matashiyar Da Aka Yi Wa Sanadin Rasa Kafa A Sakkwato

Related

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

21 hours ago
Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

2 days ago
Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

5 days ago
Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 
Siyasa

Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 

5 days ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

5 days ago
Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
Manyan Labarai

Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

5 days ago
Next Post
Wani Ya Yi Alkawarin Auren Matashiyar Da Aka Yi Wa Sanadin Rasa Kafa A Sakkwato

Wani Ya Yi Alkawarin Auren Matashiyar Da Aka Yi Wa Sanadin Rasa Kafa A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.