ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

12 Ga Yuni: Muhimman Abubuwan Da Buhari Ya Fada A Jawabinsa Na Ranar Dimokuradiyya

by Muhammad
3 years ago
12

Ranar 12 ga watan Yunin kowacce shekara ake bikin zagayowar Ranar Dimukuradiyya a Nijeriya.

An fara gudanar da bikin wannan rana ce tun daga shekarar 2002, haka kuma shugaba Muhammadu Buhari ya kara wa wannan rana karfi a shekarar 2018 bayan da ya sauya Ranar Dimokuradiyyar daga ranar 29 ga watan Mayu zuwa ranar 12 ga watan Yuni.

  • 12 Ga Yuni: Atiku, Tinubu Da Obi Da Ragowar Wasu Za Su Sanya Furanni A Kabarin Abiola
  • 2023: An Bukaci Tinubu Ya Dora Kan Irin Salon Mulkin Buhari Kwabo Da Kwabo

Aminiya-trust ta wallafa jawabin da shugaba Buhari ya gabatar a safiyar ranar Lahadi, cewa ya soma ne da bayani kan muhimmancin Ranar Dimokuradiyya inda ya jaddada muhimmancin zaben Yunin 1993 a tarihin Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Shugaba Buhari ya ce kada ’yan Nijeriya su manta da irin gudunmawa da sadaukar da kai da gawarazan dimokuradiyya suka bayar a 1993.

Ya bukaci ’yan Nijeriya da su yi koyi da kishin kasa irin na magabata a duk lokacin da za su zabi shugabanni.

LABARAI MASU NASABA

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

Shugaban ya sake tuna wa ’yan Nijeriya cewa wannan ce Ranar Dimokuradiyya ta karshe da zai yi a matsayinsa na Shugaban Kasa inda ya ce yana cike da kudirin tabbatar da cewa an zabi sabon shugaban kasa ta hanyar zabe na gaskiya da adalci.

Haka kuma Shugaba Buhari ya yaba da yadda aka gudanar da zaben fitar da gwani a kasar inda ya ce daya daga cikin abin da ya birge shi da zaben shi ne yadda mata da matasa a kusan duka jam’iyyun suka fito neman takara, “wannan alama ce da ke nuna dimokuradiyyar Nijeriya ta kara bunkasa a cikin shekara 23 da aka shafe.

“Yayin da muke shiga kakar yakin neman zabe da kuma zabe na gama gari, kada mu taba daukansa a matsayin wani alamrari na a mutu ko a yi rai, dole ne mu tuna cewa dimokuradiyya ta yi tanadin abin da mafi rinjayen kaso na alumma suke so, saboda haka dole za a samu masu nasara da masu faduwa.

Shugaban ya bayyana cewa a shekara bakwai da ya shafe kan mulki, gwamnatinsa ta yi kokari wurin gyara Dokokin Zabe da yanayin gudanar da zaben domin kare kuri’un al’umma.

Kan dai batun zaben, Shugaba Buhari ya bayyana cewa bangaren Zartarwa da Dokoki da kuma Shari’a na da kudirin ganin sun aiwatar da wadannan sauye-sauye na Dokokin zabe a yayin zaben 2023.

Shugaba Buhari ya kuma bukaci duk ’yan Nijeriya su saka wadanda rikicin ta’addanci ya rutsa da su cikin addu’a, yana mai cewa a kullum yana kwana yana tashi da bakin cikin wadanda aka yi garkuwa da su.

Ya bayar da tabbacin cewa duk hukumomin tsaron kasar na yin duk mai yiwuwa domin ceto wadanda aka sace.

“Na san cewa muna cike da damuwa kan yadda ake fama da kalubale na matsalar tsaro a sakamakon ayyukan ta’addanci, a matsayinmu na gwamnati muna aiki tukuru don shawo kan wadannan kalubale.

“Don ganin an samu biyan wannan bukata, dole kowa ya bayar da gudunmawa. Ba aikin gwamnati ba ne ita kadai, akwai bukatar dukkan yan kasa su ba rika bai wa jamian tsaro hadin kai ta hanyar mika musu rahoton duk wani mutum da ake zargi da aikata laifi ko wani motsi da basu yarda da shi ba.

“Zan karkare wannan jawabi na Ranar Dimokuradiyya, wanda kuma shi na karshe da zan yi a matsayina na Shugaban kasa, ta hanyar tabbatar muku da kudirin da na dauka na kare Najeriya da ‘yan Nijeriya daga dukkan makiya daga ciki da waje.”

Buhari ya rufe jawabansa da Yi Wa Nijeriya Addu’a.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe
Labarai

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Kwankwaso
Labarai

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
Nazari

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Next Post
12 Ga Yuni Sam Ba Ta Dace Da Ranar Dimokradiyya Ba A Nijeriya —Ra’ayin Najib Sani

12 Ga Yuni Sam Ba Ta Dace Da Ranar Dimokradiyya Ba A Nijeriya —Ra'ayin Najib Sani

LABARAI MASU NASABA

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.