• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Dan Takarar Da Ya Fi Kwarewa Za Mu Goya Wa Baya -Dattawan Arewa

by Shehu Yahaya
3 years ago
in Labarai
0
2023: Dan Takarar Da Ya Fi Kwarewa Za Mu Goya Wa Baya -Dattawan Arewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Dattawan Arewa (NEF) ta bayyana cewa a shirye take ta mara wa duk wani dan takarar kujerar shugabancin kasar a zaben 2023 baya bisa cancanta.

Shugaban kungiyar, Farfesa Ango Abdullahi, shi ne ya bayyana hakan a yayin da yake jawabi lokacin taron kaddamar da wani littaci da kungiya matasan arewa masu muradin masar da kyakkyawan shugabanci ta gudana a Kaduna.

  • Kwastam Ta Damke Mazakutar Jaki 7000 Da Miyagun Kwayoyi A Legas
  • An Shirya Tattaunawar Tiangong Tsakanin ‘Yan Sama Jannatin Sin Da Matasan Afirka Cikin Nasara

Farfesa Ango wanda shi ne shugaban taron, ya nuni da cewa arewa za ta mara wa duk wani dan takarar shugaban kasa baya ne kawai bisa la’akari da cancantarsa, da zai iya yin shugabanci cikin gaskiya, kwarewa, tausayi da tsoron Allah.

Ya tabbatar da cewa yankin zai goyi bayan dan takarar da baya neman cin gajiyar dabarun amfani da bambancin kabilanci da addini na yankin.

Farfesa Ango ya ci gaba da cewa, arewa ba za ta goyi bayan dan takarar da ya kasa gamsuwar da al’ummar cewa zai iya inganta harkokin mulki da kuma mutuncin shugabanni.

Labarai Masu Nasaba

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

An San Masu ÆŠaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

Ya ce yankin arewa za ta shiga harkokin siyasa daidai bakin gwargwado da kuma mutunta sauran ‘yan Nijeriya masu mutunta su.

Ya ce, “Mun biya farashi mai yawa a rikice-rikicen addini a arewa, kuma ba ma bukatar yin wani abu.

Rashin tsaro da durkushewar tattalin arzikinmu ba sa nuna bambanci tsakanin Musulmai da Kiristoci.

“Muna gargadin cewa wadannan yunkurin wulakanci za su gaza, saboda ba su sami wani tallafi ba a karni tarihin da ya wuce, ko kuma a baya-bayan nan.

Yayin da muka bambanta a bin gaskiya da kabilanci, tarihi, labarin kasa da kuma abubuwan da muka samu a rayuwa a matsayinmu na ‘yan Nijeriya sun haifar da tushe na zumuncin da ba za a iya lalata su ta hanyar matsananciyar siyasa ba.

“Kuri’un Arewa za su yi tasiri sosai a zaben 2023, domin mutanenmu a yanzu sun fi kowa samun hankali da fahimta yadda za su kada su.”

Farfesa Ango Abdullahi ya bayyana matasan da suka wallafa littafin a matsayin hazikan mutane da hakan ya ba shi damar goyon bayan aikin domin ganin an samu cimma nasarar gabatar da shi ga al’umma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Takara2023ArewaKwarewaMulkiZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Me Ya Sa Ba A Fara Shekarar Hijirah Da Ranar Badar Ko Ranar Cikar Wahayi Ba? (II)

Next Post

‘Muna Kira A Samar Da Jami’an Tsaro Na Yankin Arewacin Nijeriya’

Related

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato
Labarai

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

3 hours ago
An San Masu ÆŠaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu ÆŠaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

5 hours ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

7 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

8 hours ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

16 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

20 hours ago
Next Post
‘Muna Kira A Samar Da Jami’an Tsaro Na Yankin Arewacin Nijeriya’

‘Muna Kira A Samar Da Jami’an Tsaro Na Yankin Arewacin Nijeriya’

LABARAI MASU NASABA

GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

August 22, 2025
Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

August 22, 2025
Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar Nan (7)

Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar Nan (7)

August 22, 2025
An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

August 22, 2025
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

August 22, 2025
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

August 22, 2025
An San Masu ÆŠaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

An San Masu ÆŠaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

August 22, 2025
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

August 22, 2025
Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

August 22, 2025
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.