ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Dan Takarar Da Ya Fi Kwarewa Za Mu Goya Wa Baya -Dattawan Arewa

by Shehu Yahaya
4 years ago
Kwarewa

Kungiyar Dattawan Arewa (NEF) ta bayyana cewa a shirye take ta mara wa duk wani dan takarar kujerar shugabancin kasar a zaben 2023 baya bisa cancanta.

Shugaban kungiyar, Farfesa Ango Abdullahi, shi ne ya bayyana hakan a yayin da yake jawabi lokacin taron kaddamar da wani littaci da kungiya matasan arewa masu muradin masar da kyakkyawan shugabanci ta gudana a Kaduna.

  • Kwastam Ta Damke Mazakutar Jaki 7000 Da Miyagun Kwayoyi A Legas
  • An Shirya Tattaunawar Tiangong Tsakanin ‘Yan Sama Jannatin Sin Da Matasan Afirka Cikin Nasara

Farfesa Ango wanda shi ne shugaban taron, ya nuni da cewa arewa za ta mara wa duk wani dan takarar shugaban kasa baya ne kawai bisa la’akari da cancantarsa, da zai iya yin shugabanci cikin gaskiya, kwarewa, tausayi da tsoron Allah.

ADVERTISEMENT

Ya tabbatar da cewa yankin zai goyi bayan dan takarar da baya neman cin gajiyar dabarun amfani da bambancin kabilanci da addini na yankin.

Farfesa Ango ya ci gaba da cewa, arewa ba za ta goyi bayan dan takarar da ya kasa gamsuwar da al’ummar cewa zai iya inganta harkokin mulki da kuma mutuncin shugabanni.

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

Ya ce yankin arewa za ta shiga harkokin siyasa daidai bakin gwargwado da kuma mutunta sauran ‘yan Nijeriya masu mutunta su.

Ya ce, “Mun biya farashi mai yawa a rikice-rikicen addini a arewa, kuma ba ma bukatar yin wani abu.

Rashin tsaro da durkushewar tattalin arzikinmu ba sa nuna bambanci tsakanin Musulmai da Kiristoci.

“Muna gargadin cewa wadannan yunkurin wulakanci za su gaza, saboda ba su sami wani tallafi ba a karni tarihin da ya wuce, ko kuma a baya-bayan nan.

Yayin da muka bambanta a bin gaskiya da kabilanci, tarihi, labarin kasa da kuma abubuwan da muka samu a rayuwa a matsayinmu na ‘yan Nijeriya sun haifar da tushe na zumuncin da ba za a iya lalata su ta hanyar matsananciyar siyasa ba.

“Kuri’un Arewa za su yi tasiri sosai a zaben 2023, domin mutanenmu a yanzu sun fi kowa samun hankali da fahimta yadda za su kada su.”

Farfesa Ango Abdullahi ya bayyana matasan da suka wallafa littafin a matsayin hazikan mutane da hakan ya ba shi damar goyon bayan aikin domin ganin an samu cimma nasarar gabatar da shi ga al’umma.

Kwarewa
Shehu Yahaya
+ postsBio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Bayan Shehu Sani Ya Ƙalubalanci Zailani, Rikicin APC Ya Ƙara Zafi A Kaduna

MASU ALAKA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Ra'ayi Riga

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Next Post
‘Muna Kira A Samar Da Jami’an Tsaro Na Yankin Arewacin Nijeriya’

‘Muna Kira A Samar Da Jami’an Tsaro Na Yankin Arewacin Nijeriya’

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.