• English
  • Business News
Sunday, May 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: INEC Ta Samar Da Ingatattun Tsarukan Gudanar Da Tsaftataccen Zabe

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
2023: INEC Ta Samar Da Ingatattun Tsarukan Gudanar Da Tsaftataccen Zabe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yanzu da zaɓen 2023 ke ƙara kusantowa, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa bijiro da wasu ƙwararan matakai huɗu da ta yi sun tabbatar da cewa babu wata hanya da za a iya bi a yi maguɗi anl zaɓen.

Mataki na farko shi ne dabarar tantance wanda ya yi rajistar mallakar katin zaɓe sau biyu ko fiye da haka, wato ‘Biomodal Voter Accreditation System’ (BVAS).

  • Mutum Miliyan 93.5 Ne Za Su Kada Kuri’a A Zaben 2023 – INEC

Na biyu shi ne amfani da na’urar tantance adadin masu zaɓe a rumfunan zaɓe, wato ‘INEC Voter Enrollment Device’ (IVED). Shi wannan tsari ya na maganin masu satar ƙuri’a ko ɓarayin akwatin zaɓe.

Na uku shi ne manhajar tattara sakamakon zaɓen da kowa zai iya gani ido-da-ido, wato ‘INEC Result Viewing Portal’ (IRVP).

Da ya ke magana a wurin taron zaburar da matasa muhimmancin zaɓe, wanda ƙungiyar Yiaga Africa ta shirya a Inugu, Mataimakin Sakataren INEC, Injiniya Chidi Nwafor, ya ce Dokar Zaɓe ta 2022 ita ce matakin hana maguɗin zaɓe na huɗu.

Labarai Masu Nasaba

Dabarun Tinubu Sun Ƙara Kuɗaɗe A Harkar Ma’adanai Daga Naira Biliyan 6 Zuwa Biliyan 38 — Alake

Fitaccen Fastan Kaduna Rabaran Azzaman Ya Mutu A Haɗarin Mota

Saura kwana 116 a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar wakilai da na majalisar dattawa.

Idan ba a manta ba, a farkon Oktoba shi ma Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa, Farfesa Mahmood Yakubu, ya tabbatar da cewa maguɗi ba zai yiwu a zaɓen 2023 ba.

A labarin, ya ce INEC ta fito da hanyoyin kashe maguɗin zaɓe.

Yayin da hukumar ke ci gaba da tsare-tsaren gudanar da zaɓubbukan 2023, shugaban ya bugi ƙirji da cewa INEC ta samu nasarar toshe duk wata ƙofar da za a iya bi a yi maguɗi.

Da ya ke jawabi a wani taron da aka shirya a Cocin St. James na Ɗariƙar Angalika da ke Asokoro, Abuja, a kwanan baya, Yakubu ya ce INEC ta samu wannan gagarumar nasara ne ta hanyar ƙirƙiro tsarin tantance mai rajistar zaɓe na ƙeƙe-da-ƙeƙe, wato BVAS.

Yakubu, wanda Mataimakin Kakakin Yaɗa Labarai da Wayar da Kai ba hukumar, Chukwuemeka Ugboaja, ya wakilta, ya tsarin tantance mai karin rajistar hikima ce da basirar injiniyoin INEC ta kai su ga kirƙiro shi.

Ya ce BVAS zai ƙara wa INEC ƙarfin gwiwar tabbatar da cewa ta shirya zaɓe sahihi, wanda babu yadda za a iya yin maguɗi a lokacin zaɓe.

Ya ce: “Abu na biyu da zai ƙara wa zaɓen 2023 inganci shi ne sabuwar Dokar Zaɓe ta 2022. Sashe na 9 (6) ya bai wa INEC ikon daina yi wa mutane rajista kwanaki 90 kafin zaɓe. Daga nan ne kuma sai hukumar ta tankaɗe tare da tace rajistar ɗungurugum.

“Kuma mutane su fahimci cewa INEC ba ta iya soke rajistar kowa. Amma ta na da ikon soke rajistar wanda ya yi rajista sau biyu.

“Hanya ta uku da za a kawo ƙarshen maguɗin zaɓe ita ce aikawa da sakamakon zaɓe kai-tsaye ta na’urorin kafafen sadarwa na zamani daga rumfar zaɓe.

“Sannan kuma Sashe na 51 na Dokar Zaɓe ta 2021 ya nuna ƙin amincewa da sakamakon zaɓen inda adadin ƙuri’un da aka jefa a akwati su ka haura adadin yawan waɗanda aka tantance ta tsarin BVAS.

“Sannan kuma a zaɓen 2023, Sabuwar Dokar Zaɓe ta 2023 ta haramta wa INEC karɓar sakamakon da aka tilasta wa jami’in zaɓe bayyana sakamkon zaɓe.”

Ya buga misali da zaɓen sanata na Jihar Imo a 2019, wanda duk da cewa tilasta jami’in INEC aka yi ya karanta sakamakon zaɓen, amma kotu ta amince da sakamakon. Ya ce a yanzu ƙarƙashin sabuwar dokar zaɓe, hakan ba zai yiwu ba.

Daga ƙarshe ya yi kira ga manya da masu ilimi mazauna birane cewa su daure su riƙa fita su na jefa ƙuri’a a ranar zaɓe.

Ya nuna damuwa kan cewa mazauna birane, musamman masu hali da manyan ‘yan boko, ba su zuwa su na jefa ƙuri’a, duk kuwa da cewa sun san muhimmancin yin zaɓen.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

EFCC Na Binciken Ba’asin Aikin Tashar Wutar Lantarki Ta Mambila – Minista

Next Post

PDP Ta Maka APC A Kotu, Ta Nemi A Kori Shugaban APC Na Kasa Daga Mukaminsa

Related

Dabarun Tinubu Sun Ƙara Kuɗaɗe A Harkar Ma’adanai Daga Naira Biliyan 6 Zuwa Biliyan 38 — Alake
Labarai

Dabarun Tinubu Sun Ƙara Kuɗaɗe A Harkar Ma’adanai Daga Naira Biliyan 6 Zuwa Biliyan 38 — Alake

1 hour ago
Fitaccen Fastan Kaduna Rabaran Azzaman Ya Mutu A Haɗarin Mota
Labarai

Fitaccen Fastan Kaduna Rabaran Azzaman Ya Mutu A Haɗarin Mota

2 hours ago
Tsadar Farashin Ƙwai Ya Sa Ƴan Nijeriya Sun Haƙura Da Cinsa
Labarai

Tsadar Farashin Ƙwai Ya Sa Ƴan Nijeriya Sun Haƙura Da Cinsa

4 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Labarai

Tangarɗar Na’ura: JAMB Ta Sake Fitar Da Sakamakon Jarabawar UTME Ta 2025

6 hours ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

Ya Kuɓuta A Hannun ‘Yan Bindiga Bayan Shafe Kwanaki 8 Yana Gudu A Dajin Sokoto Da Neja

7 hours ago
katsina
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 5 A Katsina

8 hours ago
Next Post
PDP Ta Maka APC A Kotu, Ta Nemi A Kori Shugaban APC Na Kasa Daga Mukaminsa

PDP Ta Maka APC A Kotu, Ta Nemi A Kori Shugaban APC Na Kasa Daga Mukaminsa

LABARAI MASU NASABA

Chelsea, Man City, Newcastle Sun Samu Gurbi A Gasar Zakarun Turai Ta Baɗi

Chelsea, Man City, Newcastle Sun Samu Gurbi A Gasar Zakarun Turai Ta Baɗi

May 25, 2025
Xi Jinping Ya Taya Murnar Bude Bikin Baje Kolin Kayayyaki Na Yammacin Sin

Xi Jinping Ya Taya Murnar Bude Bikin Baje Kolin Kayayyaki Na Yammacin Sin

May 25, 2025
Dabarun Tinubu Sun Ƙara Kuɗaɗe A Harkar Ma’adanai Daga Naira Biliyan 6 Zuwa Biliyan 38 — Alake

Dabarun Tinubu Sun Ƙara Kuɗaɗe A Harkar Ma’adanai Daga Naira Biliyan 6 Zuwa Biliyan 38 — Alake

May 25, 2025
Fitaccen Fastan Kaduna Rabaran Azzaman Ya Mutu A Haɗarin Mota

Fitaccen Fastan Kaduna Rabaran Azzaman Ya Mutu A Haɗarin Mota

May 25, 2025
Ruhin Yuan Longping Ya Ba Da Tabbaci Ga Samar Da Isashen Hatsi a Nahiyar Afirka

Ruhin Yuan Longping Ya Ba Da Tabbaci Ga Samar Da Isashen Hatsi a Nahiyar Afirka

May 25, 2025
Gasar Wasanni Ta Kasa: Jihar Binuwai Ta Samu Kyaututtuka 9 Zuwa Yanzu

Gasar Wasanni Ta Kasa: Jihar Binuwai Ta Samu Kyaututtuka 9 Zuwa Yanzu

May 25, 2025
Tsadar Farashin Ƙwai Ya Sa Ƴan Nijeriya Sun Haƙura Da Cinsa

Tsadar Farashin Ƙwai Ya Sa Ƴan Nijeriya Sun Haƙura Da Cinsa

May 25, 2025
An Kaddamar Da Babban Filin Wasan Da Kasar Sin Ta Gina Wa Kasar Chadi Kyauta

An Kaddamar Da Babban Filin Wasan Da Kasar Sin Ta Gina Wa Kasar Chadi Kyauta

May 25, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

Tangarɗar Na’ura: JAMB Ta Sake Fitar Da Sakamakon Jarabawar UTME Ta 2025

May 25, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Ya Kuɓuta A Hannun ‘Yan Bindiga Bayan Shafe Kwanaki 8 Yana Gudu A Dajin Sokoto Da Neja

May 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.