• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Mun Fara Horas Da Ma’aikatan Wucin-gadi Miliyan 1.2 – INEC

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
2023: Mun Fara Horas Da Ma’aikatan Wucin-gadi Miliyan 1.2 – INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta fara aikin horas da ma’aikatan da za su yi aikin zaɓen 2023 a cikin Fabrairu da Maris.

 

Ma’aikatan na wucin-gadi su miliyan 1 ne da 265,227, kamar yadda Babban Jami’in Wayar da Kai kuma Kwamishina na INEC, Mista Festus Okoye, ya bayyana a ranar Litinin, a wurin bayar da wani horon a ranar Litinin.

  • CBN Ya Tabbatarwa INEC Samun Wadatattun Takardun Naira Don Gudanar Da Zaben 2023

Ya ce hukumar ta ɗauki wannan horaswa da muhimmanci, ganin cewa Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa, Farfesa Mahmood Yakubu ya sha alwashin tabbatar da an gudanar da sahihin zaɓe, karɓaɓɓe, kuma wanda jama’a za su yi tururuwar fita su jefa ƙuri’a.

 

Labarai Masu Nasaba

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Okoye ya ƙara cewa haka kuma wannan zaɓe mai zuwa, zaɓe ne wanda za a yi amfani da na’urar fasaha a wurin zaɓe.

 

Ya yi tsinkayen cewa aikin ofishin sa ne wanda aka ɗora wa haƙƙin shawartar Kwamishinonin Zaɓe na Jihohi (REC) da jami’an zaɓe hanyoyin da su ka fi dacewa su fahimtar da jama’a batutuwan da su ka danganci amfani da na’urorin fasaha a lokacin zaɓe.

INEC

Ya ƙara da cewa a ranakun 25 ga Fabrairu da 11 ga Maris ‘yan Nijeriya za su zaɓi shugaban ƙasa, sanatoci 109, mambobin majalisar wakilai su 360, gwamnoni 28, sai mambobin majalisar dokoki 993.

 

Ya ce mutum miliyan 93 da 469,008 ne su ka yi rajistar katin zaɓe, kuma ake sa ran za su fita su jefa ƙuri’a a ranakun 25 ga Fabrairu da 11 ga Maris.

 

Ya ce: “Zaɓen 2023 zai tafi ne a bisa tsarin amfani da na’urar fasahar zamani. INEC za ta yi amfani da na’urar tantance masu katin shaidar rajistar zaɓe, wato BVAS a dukkan rumfunan zaɓe 176,846 a ƙasar nan.

 

“Kuma INEC ta yi gwajin waɗannan na’urorin, wato BVAS ta tabbatar da ingancin su. Yanzu haka ana ci gaba da ba su lambobin tantance mai katin shaidar rajistar zaɓe, ta yadda za su kasance lambobin sun zama mabiyi da mabiyi, ko ɗaya bayan ɗaya a lokacin zaɓe.”

 

A cewar Okoye, Sashen Dokar Zaɓe na 47(2) ya tilasta cewa babu wanda zai yi zaɓe ba tare da an tantance shi na BVAS ba.

 

Ya ƙara da cewa: “Za a yi amfani da baturen zaɓe 707, 384 da su ka haɗa da mataimakan su. Sai kuma wasu ma’aikata 17,685 a matsayin turawan zaɓe masu sa-ido, jami’an tattarawa da bayyana sakamakon zaɓe su 9,620, sai kuma jami’an tsaron rumfunan zaɓe su 530,538. Ya ce gaba ɗaya idan an haɗa, sun cika 1,265,227 kenan.

 

Dukkan waɗannan su na ci gaba da samun horon sanin makamar aiki, yayin da nan da ‘yan kwanaki za a ci gaba da bayar da horon ga saura, inji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rikicin Kabilanci: An Gudanar Da Taron Yafe Wa Juna A Jihar Filato

Next Post

An Ciro Wata Mata Da Rai Daga Baraguzai Bayan Shafe Awa 52 A Turkiyya

Related

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar
Labarai

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

22 minutes ago
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo
Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

1 hour ago
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

5 hours ago
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

6 hours ago
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

8 hours ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

9 hours ago
Next Post
An Ciro Wata Mata Da Rai Daga Baraguzai Bayan Shafe Awa 52 A Turkiyya

An Ciro Wata Mata Da Rai Daga Baraguzai Bayan Shafe Awa 52 A Turkiyya

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.