• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Namadi Sambo Ya Gwangwaje Atiku Da Kyautar Ofishin Yakin Neman Zabe A Kaduna

by Muhammad
3 years ago

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, ya kaddamar da sabon ofishinsa na shiyyar Arewa maso Yamma.

Ofishin yakin neman zaben a Jihar Kaduna, wanda tsohon mataimakin shugaban kasa Namadi Sambo ya bayar a matsayin gudumawa.

  • Atiku Ya Tafi Turai Kan Harkar Kasuwanci 
  • Atiku Ya Yi Alkawarin Dawo Da Zaman Lafiya Da Sake Farfado Da Masana’antu A Jihar Kaduna

A wajen kaddamar da bude ofishin, jam’iyyar PDP ta yabawa tsohon mataimakin shugaban kasa, Namadi Sambo, bisa bayar da gudunmuwar ofishin yakin neman zaben jam’iyyar domin samun nasarar jam’iyyar a zaben 2023.

Atiku ya shaida wa magoya bayan jam’iyyar da suka taru a wajen bikin kaddamar da ofishin da su yi wa jam’iyyar aiki tukuru domin ganin ta samu nasara a zaben.

A cewarsa, duk wanda ya yi wa jam’iyyar aiki za a ba shi kyauta mai kyau bayan an kammala zabe.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

Ya ce, “Ina son in yaba wa tsohon mataimakin shugaban kasa, Namadi Sambo, bisa irin wannan karamci da ya yi wajen bayar da wannan ofishin, kowa ya yi kokari wajen ganin jam’iyyarmu ta samu nasara a zabe mai zuwa kuma ta yi nasara sosai, a wannan karon na ga hadin kan da aka samu a cikin jam’iyyar da jajircewar ‘ya’yan jam’iyyar na jihar Kaduna na kishin ganin mun yi nasarar a jihar da zaben ‘yan majalisun tarayya da na shugaban kasa.

“Ina tabbatar muku cewa jam’iyya a matakin kasa za ta ba ku goyon baya da kuma tabbatar da nasara a jiha a kowane mataki, idan kun yi wa jam’iyyar aiki da kyau kuma kuka yi wa Atiku aiki da kyau kuma ya ci zaben shugaban kasa, za a ba ku kyauta mai tsoka. .”

Tsohon mataimakin shugaban kasa Sambo, wanda ya yi magana tun farko, ya ce ‘ya’yan jam’iyyar a jihar Kaduna a shirye suke su ba Atiku gudunmawa a jihar.

Ya ce sabon ofishin da aka bayar zai zama ofishin jam’iyyar a shiyyar Arewa maso Yamma da kuma jihar.

“Jihar Kaduna a shirye ta ke ta zabi PDP a zabe mai zuwa a 2023, mun riga mun yi aiki don ganin nasararku da jam’iyya a zabe mai zuwa.

“Babu shakka za mu yi nasara a wannan zabe domin kowa za a yi aiki tare domin samun nasara,” inji Sambo.

Har ila yau, a wajen taron, Amb Usman Elkudan, daya daga cikin makusantan tsohon mataimakin shugaban kasa, Namadi Sambo, ya ce wannan mafarin ne na goyon bayan da maigidansa ya yi wa takarar Atiku Abubakar.

Ya yi alkawarin za su ci zabe a kowane mataki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu
Siyasa

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

October 16, 2025
Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson
Manyan Labarai

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

October 16, 2025
Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Next Post
Hu Hailan: Masaniyar Kasar Sin Da Ta Kai Matsayin Koli A Fannin Kimiyyar Kwakwalwa Da Jijiyoyi A Duniya

Hu Hailan: Masaniyar Kasar Sin Da Ta Kai Matsayin Koli A Fannin Kimiyyar Kwakwalwa Da Jijiyoyi A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
NAWIA

Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

October 16, 2025
Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

October 16, 2025
Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

October 16, 2025
Tinubu

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.