• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Namadi Sambo Ya Gwangwaje Atiku Da Kyautar Ofishin Yakin Neman Zabe A Kaduna

by Muhammad
3 years ago

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, ya kaddamar da sabon ofishinsa na shiyyar Arewa maso Yamma.

Ofishin yakin neman zaben a Jihar Kaduna, wanda tsohon mataimakin shugaban kasa Namadi Sambo ya bayar a matsayin gudumawa.

  • Atiku Ya Tafi Turai Kan Harkar Kasuwanci 
  • Atiku Ya Yi Alkawarin Dawo Da Zaman Lafiya Da Sake Farfado Da Masana’antu A Jihar Kaduna

A wajen kaddamar da bude ofishin, jam’iyyar PDP ta yabawa tsohon mataimakin shugaban kasa, Namadi Sambo, bisa bayar da gudunmuwar ofishin yakin neman zaben jam’iyyar domin samun nasarar jam’iyyar a zaben 2023.

Atiku ya shaida wa magoya bayan jam’iyyar da suka taru a wajen bikin kaddamar da ofishin da su yi wa jam’iyyar aiki tukuru domin ganin ta samu nasara a zaben.

A cewarsa, duk wanda ya yi wa jam’iyyar aiki za a ba shi kyauta mai kyau bayan an kammala zabe.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Ya ce, “Ina son in yaba wa tsohon mataimakin shugaban kasa, Namadi Sambo, bisa irin wannan karamci da ya yi wajen bayar da wannan ofishin, kowa ya yi kokari wajen ganin jam’iyyarmu ta samu nasara a zabe mai zuwa kuma ta yi nasara sosai, a wannan karon na ga hadin kan da aka samu a cikin jam’iyyar da jajircewar ‘ya’yan jam’iyyar na jihar Kaduna na kishin ganin mun yi nasarar a jihar da zaben ‘yan majalisun tarayya da na shugaban kasa.

“Ina tabbatar muku cewa jam’iyya a matakin kasa za ta ba ku goyon baya da kuma tabbatar da nasara a jiha a kowane mataki, idan kun yi wa jam’iyyar aiki da kyau kuma kuka yi wa Atiku aiki da kyau kuma ya ci zaben shugaban kasa, za a ba ku kyauta mai tsoka. .”

Tsohon mataimakin shugaban kasa Sambo, wanda ya yi magana tun farko, ya ce ‘ya’yan jam’iyyar a jihar Kaduna a shirye suke su ba Atiku gudunmawa a jihar.

Ya ce sabon ofishin da aka bayar zai zama ofishin jam’iyyar a shiyyar Arewa maso Yamma da kuma jihar.

“Jihar Kaduna a shirye ta ke ta zabi PDP a zabe mai zuwa a 2023, mun riga mun yi aiki don ganin nasararku da jam’iyya a zabe mai zuwa.

“Babu shakka za mu yi nasara a wannan zabe domin kowa za a yi aiki tare domin samun nasara,” inji Sambo.

Har ila yau, a wajen taron, Amb Usman Elkudan, daya daga cikin makusantan tsohon mataimakin shugaban kasa, Namadi Sambo, ya ce wannan mafarin ne na goyon bayan da maigidansa ya yi wa takarar Atiku Abubakar.

Ya yi alkawarin za su ci zabe a kowane mataki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
Siyasa

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
Next Post
Hu Hailan: Masaniyar Kasar Sin Da Ta Kai Matsayin Koli A Fannin Kimiyyar Kwakwalwa Da Jijiyoyi A Duniya

Hu Hailan: Masaniyar Kasar Sin Da Ta Kai Matsayin Koli A Fannin Kimiyyar Kwakwalwa Da Jijiyoyi A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 3, 2025
Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

November 3, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano

November 3, 2025
Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT

Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT

November 3, 2025
Sabon Muƙaddashin Shugaban PDP Ya Sha Alwashin Maido Da Martabar Jam’iyyar Kafin 2027

Sabon Muƙaddashin Shugaban PDP Ya Sha Alwashin Maido Da Martabar Jam’iyyar Kafin 2027

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.