ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Tinubu Da Atiku Ba Za Su Iya Gyara Nijeriya Ba — Ango Abdullahi

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Ango

Jigo a cikin kungiyar dattawan arewa (NEF), Farfesa Ango Abdullahi ya bayyana cewa a halin yanzu da ake ciki, manyan ‘yan takarar shugaban kasa ba za su taba iya gyara Nijeriya ba.

Ya ce a cikin ‘yan takarar shugaban kasa da ke da su a halin yanzu, gwara ‘yan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar LP, Mista Peter Obi da na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Masu Kwankwaso kila za su iya tabuka wani abu, amma ‘yan takatar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu da na PDP, Atiku Abubakar ba za su iya tabuka komi ba.

  • NNPP Ta Kaddamar Da Kwamitin Sulhu Da Zaman Lafiya A Neja

Ya dai jaddada cewa wadannan ‘yan takara sun shafe shakara da shekaru suna gudanar da siyasa a Nijeriya ba tare da kawo wani sauyi ba. Ya ce da jam’iyyar APC ta bai wa Mataimakin Shugaban Kasa, Yemi Osinbajo takara zai iya cewa gwara-gwara, haka ma da PDP ta bai wa tsohon ma’aikacin banki, Mohammed Hayatu-Deen takara da zai iya ganin za a samun kwarrun ‘yan takarar shugabanin kasa.

ADVERTISEMENT

Ango Abdullahi ya kara da cewa ba zai taba goyon bayan daya daga cikin wadannan ‘yan takararan shugaban kasa ba. Ya ce yana kira ga ‘yan Nijeriya su tashi tsaye wajen kalubalantar wadannan ‘yan takarar shugaban kasa domin ganin daya daga cikinsu bai hau karagar mulki ba a 2023.

Jigon ya bayyana hakan ne lokacin da yake zantawa da ‘yan jarida ta wayar salula a cikin makon da ya gabata.
Ya ce, “Har hanzu bai ga wani dan takara da zai iya gyara Nijeriya ba. ‘Yan takarar da muka da su a yanzu ba za su iya tabuka komi ba. Domin ta yaya za a iya cewa Tinubu da Atiku za su iya gyara Nijeriya.?
“Sun kashe shekaru 25 zuwa 30 suna gudanar da harkokin siyasa, amma babu wani abu da suka taba yi na gyara Nijeriya. To me za mu yi da wadannan ‘yan takara?
“Akwai mutanen da suka cancanta amma ba su aka bai wa takara ba saboda tsarin siyasan a gurbace take,” in ji shi.
Ya ci gaba da cewa yana kira ga ‘yan Nijeriya da su sani akwai matsaloli a Nijeriya kuma dole su da kansu ne za su iya samar wa kansu mafita a kan wadannan matsaloli wajen zaben shugaban kasan da ya dace a 2023.

LABARAI MASU NASABA

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC

‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC

December 19, 2025
‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama

December 19, 2025
Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027
Tambarin Dimokuradiyya

NNPP Ta Buƙaci INEC Ta Yi Watsi Da Tarukan Jam’iyyar Da Kwankwaso Zai Jagoranta

November 28, 2025
Next Post
Buhari Ya Ce Ba Zai Nemi Wa’adi Na Uku Ba

Yadda Buhari Ya Dakile Barazanar Da APC Ke Fuskanta A Majalisar Dattawa

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.