• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Tinubu Da Atiku Ba Za Su Iya Gyara Nijeriya Ba — Ango Abdullahi

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Ango

Jigo a cikin kungiyar dattawan arewa (NEF), Farfesa Ango Abdullahi ya bayyana cewa a halin yanzu da ake ciki, manyan ‘yan takarar shugaban kasa ba za su taba iya gyara Nijeriya ba.

Ya ce a cikin ‘yan takarar shugaban kasa da ke da su a halin yanzu, gwara ‘yan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar LP, Mista Peter Obi da na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Masu Kwankwaso kila za su iya tabuka wani abu, amma ‘yan takatar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu da na PDP, Atiku Abubakar ba za su iya tabuka komi ba.

  • NNPP Ta Kaddamar Da Kwamitin Sulhu Da Zaman Lafiya A Neja

Ya dai jaddada cewa wadannan ‘yan takara sun shafe shakara da shekaru suna gudanar da siyasa a Nijeriya ba tare da kawo wani sauyi ba. Ya ce da jam’iyyar APC ta bai wa Mataimakin Shugaban Kasa, Yemi Osinbajo takara zai iya cewa gwara-gwara, haka ma da PDP ta bai wa tsohon ma’aikacin banki, Mohammed Hayatu-Deen takara da zai iya ganin za a samun kwarrun ‘yan takarar shugabanin kasa.

Ango Abdullahi ya kara da cewa ba zai taba goyon bayan daya daga cikin wadannan ‘yan takararan shugaban kasa ba. Ya ce yana kira ga ‘yan Nijeriya su tashi tsaye wajen kalubalantar wadannan ‘yan takarar shugaban kasa domin ganin daya daga cikinsu bai hau karagar mulki ba a 2023.

Jigon ya bayyana hakan ne lokacin da yake zantawa da ‘yan jarida ta wayar salula a cikin makon da ya gabata.
Ya ce, “Har hanzu bai ga wani dan takara da zai iya gyara Nijeriya ba. ‘Yan takarar da muka da su a yanzu ba za su iya tabuka komi ba. Domin ta yaya za a iya cewa Tinubu da Atiku za su iya gyara Nijeriya.?
“Sun kashe shekaru 25 zuwa 30 suna gudanar da harkokin siyasa, amma babu wani abu da suka taba yi na gyara Nijeriya. To me za mu yi da wadannan ‘yan takara?
“Akwai mutanen da suka cancanta amma ba su aka bai wa takara ba saboda tsarin siyasan a gurbace take,” in ji shi.
Ya ci gaba da cewa yana kira ga ‘yan Nijeriya da su sani akwai matsaloli a Nijeriya kuma dole su da kansu ne za su iya samar wa kansu mafita a kan wadannan matsaloli wajen zaben shugaban kasan da ya dace a 2023.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Buhari Ya Ce Ba Zai Nemi Wa’adi Na Uku Ba

Yadda Buhari Ya Dakile Barazanar Da APC Ke Fuskanta A Majalisar Dattawa

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.