• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Za A Fara Shirye-shiryen Aikin Hajji Ranar 21 Ga Disamba – NAHCON

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
2023: Za A Fara Shirye-shiryen Aikin Hajji Ranar 21 Ga Disamba – NAHCON
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Kasa (NAHCON), Alhaji Zikrullah Kunle Hassan, ya sanar da cewa, za a fara shirye-shiryen Hajjin shekarar 2023 a ranar 21 ga watan Disamba.

Da yake jawabi a wajen taron masu ruwa da tsakin bayan aikin Hajji na 2022 da aka gudanar a babban masallacin kasa da ke Abuja, Hassan ya ce za a fara shirye-shiryen tsakanin NAHCON da ma’aikatar Hajji da Umrah ta Saudiyya a ranar.

  • Kwanturola-Janar Na NIS Ya Amince Da Nadin Tony Akuneme A Matsayin Sabon Kakakin Hukumar Na Kasa
  • Subul Da Bakan Tinubu: Alamu Ne Na Ba Zai Iya Shugabancin Nijeriya Ba- Dino Melaye

A cewarsa, ya zama wajibi ga masu ruwa da tsaki su mayar da hankali wajen yi tsare-tsare da tsaftar aikin Hajjin badi da nufin neman yardar Allah.

“Hajjin 2023 ya kusanto, ya kamata mu mai da hankali kan tsare-tsare mai kyau da kuma taka tsantsan tare da sanin cewa burinmu shi ne mu faranta wa Allah ta hanyar mahajjatanmu da suka ba da jari mai yawa da nufin bauta wa Ubangijinsu kawai.

“Bugu da kari, ina mai farin cikin sanar da ku cewa, sabanin aikin Hajjin da ya gabata da aka fara shirye-shiryen a makare saboda rashin samun bayanai, ma’aikatar Hajji da Umra ta sanar da mu cewa, za a fara shirye-shiryen aikin Hajjin 2023 a wani taro ta hanyar sadarwar bidiyo. wanda aka shirya gudanarwa a ranar 21 ga Disamba 2022 tsakanin Hukumar Alhazai ta Nijeriya da ma’aikatar,” in ji shugaban.

Labarai Masu Nasaba

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Ya sanar da cewa NAHCON ta shirya gudanar da aikin Hajjin shekarar 2023 a kan tsarin tanadin aikin Hajji da kuma tsarin biyan kudi na yau da kullun.

“Manufarmu ta aikin Hajji 2023 ita ce kiyaye matsayin da ake da shi; wato gudanar da HSS daidai gwargwado tare da biyan kudaden da za ku je, kamar yadda aka yi na aikin Hajjin bana.”

Ya bayyana cewa taron masu ruwa da tsaki an shirya shi ne domin hada masu ruwa da tsaki a harkar Hajjin Nijeriya da nufin yin nazari tare da duba aikin Hajjin bana tare da samar da mafita don ingantawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Aikin HajjiAlhazaiHajiNAHCONSaudiyyaShirye-shiryeUmrah
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwanturola-Janar Na NIS Ya Amince Da Nadin Tony Akuneme A Matsayin Sabon Kakakin Hukumar Na Kasa

Next Post

Xi Ya Yi Kira Da Dunkule Tattalin Arzikin Asia Da Pasifik Yayin Da Ake Fuskantar Kalubale

Related

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

2 hours ago
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato
Manyan Labarai

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

6 hours ago
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai
Manyan Labarai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

12 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

1 day ago
Sojoji Sun Kwato Makamai Da Babura, Sun Ceto Mutane 3 A Kaduna 
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Bindiga Ɗauke Da Makamai A Jihar Filato

1 day ago
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

2 days ago
Next Post
Xi Ya Yi Kira Da Dunkule Tattalin Arzikin Asia Da Pasifik Yayin Da Ake Fuskantar Kalubale

Xi Ya Yi Kira Da Dunkule Tattalin Arzikin Asia Da Pasifik Yayin Da Ake Fuskantar Kalubale

LABARAI MASU NASABA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

September 6, 2025
Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

September 6, 2025
Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

September 6, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

September 6, 2025
Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

September 6, 2025
Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

September 6, 2025
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

September 6, 2025
Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

September 6, 2025
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.