ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

by Abubakar Sulaiman
10 months ago
Zamfara

Shugaban ƙungiyar Fulani makiyaya ta ƙasa (MACBAN), Baba Othman Ngelzarma, ya bayyana cewa Musulmin da suka rasa rayukansu a Zamfara, da Katsina da Sokoto sun ninka adadin Kiristocin da aka kashe a tsakiyar Nijeriya (Middle Belt). Ya yi wannan bayani ne a tattaunawarsa da gidan talabijin ɗin Channels, yana mai ƙalubalantar iƙirarin da ke nuna cewa ana kai wa Kiristoci hari ne musamman a rikice-rikicen da ke faruwa a sassa daban-daban na ƙasar.

Ya ce matsalar tsaro ta rikiɗe zuwa rikici mai cike da rikitarwa da ya ƙunshi bambancin ƙabila, da addini, da rikicin manoma da makiyaya, wanda ya ƙara haifar da ta’addanci, da garkuwa da mutane da kashe-kashe.

  • Kungiyar Fulani Ta MACBAN Ta Nesanta Kanta Daga Zanga-zangar Matasa
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

Ngelzarma ya ce rikice-rikicen ba yanayi ɗaya suke da shi , domin suna bambanta daga wuri zuwa wuri. Ya tunasar da harin 2017 a Sardauna, Taraba, yankin da Kiristoci suka fi yawa, inda sama da makiyaya 700 aka kashe cikin kwanaki biyu, yana mai tambaya kan dalilin da ya sa ba a duba irin wannan adadi da biyu. A Benue kuwa, ya ce tashin hankali ya karu tun daga shekarar 2014 lokacin aiwatar da dokar hana kiwo a fili, wanda ya kara tayar da kura tsakanin manoma da makiyaya a jihar da Kiristoci ke da rinjaye.

ADVERTISEMENT

A jihar Filato, Ngelzarma ya ce rikicin ya fi kama da matsalar ’yan asali da masu shigowa, amma ba rikicin addini kai tsaye ba. Ya zargi gwamnatin jihar ta yanzu da ƙara ruruta wutar rikici a Mangu, yana mai cewa lamarin bai kai haka ba a gwamnatocin baya. Ya bayyana cewa makiyaya sun daɗe suna fuskantar hare-hare a yankin, wanda ya saɓa da labarin da ake yaɗawa cewa sune ke kai hari.

Game da Boko Haram, ya ce kashi 90 cikin 100 na waɗanda suka mutu Musulmai ne, duk da cewa jama’a da dama suna ganin Kiristoci ne ake kai wa farmaki. Ya ce hankalin duniya ya fi karkata kan sace-sacen Chibok ne saboda yankin Kiristoci ne, alhali mafi yawan ɗaliban Dapchi da aka sace Musulmai ne. Ya yi nuni da cewa hakan ya nuna rikicin ya fi rikitarwa fiye da yadda ake yaɗawa.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

Ngelzarma ya kuma ce mutanen da suka mutu a Zamfara, da Katsina da Sokoto sun ninka na tsakiya Nijeriya, kuma mafi yawansu Musulmi ne. Ya buƙaci a kalli matsalar tsaron Nijeriya da idon basira da fahimtar bangarori da dama, yana mai cewa idan za a yi hukunci kan rikicin, ya kamata a kira shi da kisa bil’adama gaba ɗaya, ba kisan addini guda ɗaya ba.

Zamfara
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne

Kalubalantar Ka’idar "Kasar Sin Daya Tak A Duniya" Tamkar Wasa Da Wuta Ne

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.