ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

by Abubakar Sulaiman
8 months ago
Zamfara

Shugaban ƙungiyar Fulani makiyaya ta ƙasa (MACBAN), Baba Othman Ngelzarma, ya bayyana cewa Musulmin da suka rasa rayukansu a Zamfara, da Katsina da Sokoto sun ninka adadin Kiristocin da aka kashe a tsakiyar Nijeriya (Middle Belt). Ya yi wannan bayani ne a tattaunawarsa da gidan talabijin ɗin Channels, yana mai ƙalubalantar iƙirarin da ke nuna cewa ana kai wa Kiristoci hari ne musamman a rikice-rikicen da ke faruwa a sassa daban-daban na ƙasar.

Ya ce matsalar tsaro ta rikiɗe zuwa rikici mai cike da rikitarwa da ya ƙunshi bambancin ƙabila, da addini, da rikicin manoma da makiyaya, wanda ya ƙara haifar da ta’addanci, da garkuwa da mutane da kashe-kashe.

  • Kungiyar Fulani Ta MACBAN Ta Nesanta Kanta Daga Zanga-zangar Matasa
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

Ngelzarma ya ce rikice-rikicen ba yanayi ɗaya suke da shi , domin suna bambanta daga wuri zuwa wuri. Ya tunasar da harin 2017 a Sardauna, Taraba, yankin da Kiristoci suka fi yawa, inda sama da makiyaya 700 aka kashe cikin kwanaki biyu, yana mai tambaya kan dalilin da ya sa ba a duba irin wannan adadi da biyu. A Benue kuwa, ya ce tashin hankali ya karu tun daga shekarar 2014 lokacin aiwatar da dokar hana kiwo a fili, wanda ya kara tayar da kura tsakanin manoma da makiyaya a jihar da Kiristoci ke da rinjaye.

ADVERTISEMENT

A jihar Filato, Ngelzarma ya ce rikicin ya fi kama da matsalar ’yan asali da masu shigowa, amma ba rikicin addini kai tsaye ba. Ya zargi gwamnatin jihar ta yanzu da ƙara ruruta wutar rikici a Mangu, yana mai cewa lamarin bai kai haka ba a gwamnatocin baya. Ya bayyana cewa makiyaya sun daɗe suna fuskantar hare-hare a yankin, wanda ya saɓa da labarin da ake yaɗawa cewa sune ke kai hari.

Game da Boko Haram, ya ce kashi 90 cikin 100 na waɗanda suka mutu Musulmai ne, duk da cewa jama’a da dama suna ganin Kiristoci ne ake kai wa farmaki. Ya ce hankalin duniya ya fi karkata kan sace-sacen Chibok ne saboda yankin Kiristoci ne, alhali mafi yawan ɗaliban Dapchi da aka sace Musulmai ne. Ya yi nuni da cewa hakan ya nuna rikicin ya fi rikitarwa fiye da yadda ake yaɗawa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Ngelzarma ya kuma ce mutanen da suka mutu a Zamfara, da Katsina da Sokoto sun ninka na tsakiya Nijeriya, kuma mafi yawansu Musulmi ne. Ya buƙaci a kalli matsalar tsaron Nijeriya da idon basira da fahimtar bangarori da dama, yana mai cewa idan za a yi hukunci kan rikicin, ya kamata a kira shi da kisa bil’adama gaba ɗaya, ba kisan addini guda ɗaya ba.

Zamfara
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata
  • Abubakar Sulaiman
    Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

MASU ALAKA

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi
Manyan Labarai

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci
Manyan Labarai

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Next Post
Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne

Kalubalantar Ka’idar "Kasar Sin Daya Tak A Duniya" Tamkar Wasa Da Wuta Ne

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.