ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

by Abubakar Sulaiman
7 months ago
Zamfara

Shugaban ƙungiyar Fulani makiyaya ta ƙasa (MACBAN), Baba Othman Ngelzarma, ya bayyana cewa Musulmin da suka rasa rayukansu a Zamfara, da Katsina da Sokoto sun ninka adadin Kiristocin da aka kashe a tsakiyar Nijeriya (Middle Belt). Ya yi wannan bayani ne a tattaunawarsa da gidan talabijin ɗin Channels, yana mai ƙalubalantar iƙirarin da ke nuna cewa ana kai wa Kiristoci hari ne musamman a rikice-rikicen da ke faruwa a sassa daban-daban na ƙasar.

Ya ce matsalar tsaro ta rikiɗe zuwa rikici mai cike da rikitarwa da ya ƙunshi bambancin ƙabila, da addini, da rikicin manoma da makiyaya, wanda ya ƙara haifar da ta’addanci, da garkuwa da mutane da kashe-kashe.

  • Kungiyar Fulani Ta MACBAN Ta Nesanta Kanta Daga Zanga-zangar Matasa
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

Ngelzarma ya ce rikice-rikicen ba yanayi ɗaya suke da shi , domin suna bambanta daga wuri zuwa wuri. Ya tunasar da harin 2017 a Sardauna, Taraba, yankin da Kiristoci suka fi yawa, inda sama da makiyaya 700 aka kashe cikin kwanaki biyu, yana mai tambaya kan dalilin da ya sa ba a duba irin wannan adadi da biyu. A Benue kuwa, ya ce tashin hankali ya karu tun daga shekarar 2014 lokacin aiwatar da dokar hana kiwo a fili, wanda ya kara tayar da kura tsakanin manoma da makiyaya a jihar da Kiristoci ke da rinjaye.

ADVERTISEMENT

A jihar Filato, Ngelzarma ya ce rikicin ya fi kama da matsalar ’yan asali da masu shigowa, amma ba rikicin addini kai tsaye ba. Ya zargi gwamnatin jihar ta yanzu da ƙara ruruta wutar rikici a Mangu, yana mai cewa lamarin bai kai haka ba a gwamnatocin baya. Ya bayyana cewa makiyaya sun daɗe suna fuskantar hare-hare a yankin, wanda ya saɓa da labarin da ake yaɗawa cewa sune ke kai hari.

Game da Boko Haram, ya ce kashi 90 cikin 100 na waɗanda suka mutu Musulmai ne, duk da cewa jama’a da dama suna ganin Kiristoci ne ake kai wa farmaki. Ya ce hankalin duniya ya fi karkata kan sace-sacen Chibok ne saboda yankin Kiristoci ne, alhali mafi yawan ɗaliban Dapchi da aka sace Musulmai ne. Ya yi nuni da cewa hakan ya nuna rikicin ya fi rikitarwa fiye da yadda ake yaɗawa.

LABARAI MASU NASABA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Ngelzarma ya kuma ce mutanen da suka mutu a Zamfara, da Katsina da Sokoto sun ninka na tsakiya Nijeriya, kuma mafi yawansu Musulmi ne. Ya buƙaci a kalli matsalar tsaron Nijeriya da idon basira da fahimtar bangarori da dama, yana mai cewa idan za a yi hukunci kan rikicin, ya kamata a kira shi da kisa bil’adama gaba ɗaya, ba kisan addini guda ɗaya ba.

Zamfara
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
  • Abubakar Sulaiman
    Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
  • Abubakar Sulaiman
    Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka
  • Abubakar Sulaiman
    Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

MASU ALAKA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Next Post
Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne

Kalubalantar Ka’idar "Kasar Sin Daya Tak A Duniya" Tamkar Wasa Da Wuta Ne

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.