• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

by Yusuf Shuaibu
3 weeks ago
in Labarai
0
2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan siyasa da magoya bayansu sun ci gaba da watsi da gargadin da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta kasa (INEC) ta yi na gudanar da yakin neman zaben 2027.

Duk da umarnin da INEC ta bayar, siyasa tana kara yin zafi a tsakanin masu neman takara da magoya bayansu, yayin da suke kara daukar matakai na tallata burikansu da yin sharyi kan zaben 2027. Yanayin siyasa na kara zafafa a daidai lokacin da ya rage saura shekara biyu a yi zabe a Nijeriya.

Manyan ‘yan siyasa sun fara yin bayani da ke bayyana aniyarsu ta tsayawa takara, yayin da suke kuma neman goyon baya ga masu ruwa da tsaki daban-daban.

Musamman a matakin kasa, jam’iyyar APC mai mulki ta amince da Shugaba Bola Tinubu a matsayin dan takarar shugaban kasa guda daya tilo a zaben 2027, bayan samun goyon baya daga manyan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar, wato kwamitin zartarwa na kasada kuma na yankuna.

A taron kwamitin zartarwa na jam’iyyar da aka gudanar a ranar 26 ga Fabrairu, 2025, APC ta amince da tazarcen Shugaba Tinubu.

Labarai Masu Nasaba

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

A wannan rana, shugaban kungiyar gwamnonin APC kuma Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma, ya gabatar da kudrin goyon bayan tazarcen Tinubu. Nan take tsohon gwamnan Jihar Edo da kuma dan majalisar dattawa, Sanata Adams Oshiomhole ya amince da kudirin.

Bayan wata uku, kwamitin gudanarwa na kasa na jam’iyyar APC ya bayyana shugaban kasa Tinubu a matsayin dan takarar daya tilo na shugaban kasa a zaben 2027.

Haka nan a taron kungiyar gwamnonin APC da ‘yan majalisaun tarayya na jam’iyyar sun amince da Shugaba Tinubu a matsayin dan takararsu na shugaban kasa a zaben 2027.

Kazalika, dan takarar shugaban kasar na jam’iyyar LP a 2023, Peter Obi, ya tabbatar da niyyarsa na sake tsayawa takarar shugaban kasa a 2027, tare da alkawarin yin wa’adi guda na shekaru hudu idan aka zabe shi.

Obi ya bayyana hakan ne a shafinsa na Tuwita, inda ya amsa tambayoyin daga masu goyon baya a gida Nijeriya da kuma kasashen waje. Tsohon gwamnan Jihar Anambra ya yi alkawarin sake tsayawa takarar shugaban kasa a 2027.

Hak kuma, tsohon ministan sufuri, Chibuike Amaechi, ya bayyana niyyarsa ta takarar shugabancin kasa a 2027, yana bayyana kwarin gwiwar cewa zai iya kayar da Shugaba Tinubu a zaben 2027, idan ya samu tikitin tsayawa takarar shugaban kasa a jam’iyyar ADC.

Amaechi, ya bayyana hakan ne a yayin tattaunawa da aka yi da shi a Shafin Tuwita, ya roki jam’iyyar ADC da su ba shi tikitin takarar shugaban kasa, yana mai jaddada cewa shi ya san lagon karya Shugaba Tinubu da jam’iyyarsa ta APC mai mulki.

Wani bidiyon da ake yadawa kwanan nan game da yiwuwar neman takarar shugaban kasa a 2027 na tsohon dan takarar jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar. Masu sharhi da yawa sun fassara wannan bidiyon a matsayin wata alama ta nufin sake fitowa takara. Duk da haka, mai ba shi shawara kan harkokin yada labarai, Paul Ibe, ya musanta ikirarin, yana mai cewa bidiyon an dauke shi ne a 2022, kafin zaben fid da gwani na PDP.

A halin yanzu, a yankin arewa ta tsakiyar, kungiyar shugabannin matasa ta goyi bayan shahararren dan kasuwa, Dakta Gbenga Olawepo-Hashim, a matsayin dan takararsu na shugaban kasa a 2027.

Sun bayyana boyon bayan nasu ne a lokacin taron manema labarai a Abuja, wanda kungiyar matasa na arewa tsakiya (YANCP) ta shirya, ta kasance wata kungiya da ke nuna goyon bayan shugabanci ya tsaya a yankin arewa ta tsakiya a 2027.

Sashe na 94(1) na dokar zabe ta 2022, wanda ya ce jam’iyyun siyasa ba za su fara gudanar da yakin neman zabe ba a bainar jama’a har sai kwanaki 150 kafin ranar zabe kuma ba su wuce sa’o’i 24 kafin wannan ranar ba.

Babban sakataren yada labarai na INEC, Rotimi Oyekanmi, ya shaida wa LEADERSHIP cewa rashin dacewa da kuma rashin bin doka ne ga kowace jam’iyya ta siyasa ta fara gudanar da yakin neman zaben 2027 a wannan lokacin, wanda hakan ya saba wa dokar zabe ta 2022.

“Babu wani tanadi na musamman a cikin dokar zabe ta 2022 da ke haramta goyon bayan ‘yan takara a wurin mutane da kungiyoyi wajen zabe.

“A karkashin sashe na 94(1) na dokar zabe ta 2022, jam’iyyun siyasa ba za su fara yakin neman zabe ba har sai ya rage saura kwana 150 kafin ranar zabe kuma za a dakata a kafin awanni 24 kafin wannan rana.

“Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ba ta saki jadawalin ayyukan zaben 2027 ba, wanda zai bayyana lokacin kamfen ga jam’iyyun siyasa a fili. Saboda haka, zai zama saba wa doka ga kowace jam’iyya ta fara yakin neman zaben 2027 a wannan lokaci,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Next Post

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Related

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

2 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

10 hours ago
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

12 hours ago
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu
Labarai

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

13 hours ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

14 hours ago
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

17 hours ago
Next Post
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.