• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

by Abubakar Sulaiman
7 days ago
in Labarai
0
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Kaduna ta cafke mutane shida da ake zargi da aikata garkuwa da mutane, tare da ƙwato makamai daga hannunsu. An samu nasarar ne sakamakon atisayen haɗin gwuiwa da ‘yansanda suka gudanar a sassan jihohin Kaduna da Zamfara.

  • Tsoffin Ƴansanda Sun Fara Zanga-Zangar Ƙuncin Rayuwa A Abuja
  • Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

Kakakin Rundunar ‘Yansanda ta Kaduna, DSP Mansir Hassan, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa cewa lamarin ya samo asali ne daga wani rahoton gaggawa da wani mazaunin Ungwar Ninzom a Jagindi Tasha, ƙaramar hukumar Jama’a ya bayar ranar 22 ga Fabrairu, 2025, inda ya sanar da sace ɗansa, Hussaini Ibrahim, da wasu ‘yan bindiga suka yi.

Bayan samun rahoton, jami’an Ƴansanda daga sashin Kafanchan suka bazama don farautar masu garkuwa da mutanen. Koda yake an ce masu laifin sun tsere a farko, an ceto Hussaini daga dajin da ke kusa da yankin bayan kwana biyu, duk da cewa yana da raunin harbin bindiga a ƙafa. An ba shi kulawa a asibiti sannan aka mayar da shi ga iyalansa.

Bincike ya kai ga kama mutane huɗu: Umar Yusuf Jabiri (30), da Buhari Muhammad wanda aka fi sani da “General” (31), da Ahmadu Nasiru (51), da Zakari Saleh (50) — dukkansu mazauna Jagindi Tasha da Gidan Waya. Jami’an tsaro sun ƙwato bindiga AK-47 guda ɗaya da kuma wasu bindigogi uku ƙirar gida daga hannunsu.

A wani ci gaba kuma, bisa sahihan bayanan leƙen asiri, rundunar sashin yaƙi da garkuwa da mutane ƙarƙashin jagorancin CSP Sani Zuntu, ta gano wani kaya mai ɗauke da bindiga ƙirar AK-47 da aka ɓoye cikin buhu daga Jos, Jihar Filato zuwa Gusau, Jihar Zamfara.

Labarai Masu Nasaba

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Hakan ya haifar da cafke Abdulmumin Sani da Naziru Musa a Gusau, inda ake zargin sun je karɓar bindigar. Rundunar ta ce za a gurfanar da su kotu bayan kammala bincike. Kwamishinan Ƴansanda na jihar, CP Rabiu Muhammad, ya yaba da ƙwazon jami’an da suka gudanar da waɗannan atisayen tare da tabbatar wa da jama’a cewa rundunar ba za ta yi ƙasa a gwuiwa ba wajen kawar da ‘yan ta’adda daga jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KadunaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

Next Post

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Related

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Labarai

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

4 hours ago
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Labarai

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

7 hours ago
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto
Labarai

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

7 hours ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

9 hours ago
Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50
Labarai

Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

10 hours ago
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO
Manyan Labarai

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

10 hours ago
Next Post
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

LABARAI MASU NASABA

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

August 2, 2025
Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

August 2, 2025
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

August 2, 2025
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

August 2, 2025
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

August 2, 2025
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

August 2, 2025
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

August 2, 2025
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.