• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

by Abubakar Abba
2 months ago
Cocoa

Akwai yiwuwar Nijeriya ta gaza samun damar fitar da Cocoa da ake nomawa a kasar zuwa kasuwannin Tarayyar Turai (EU).

Hakan ka iya faruwa ne, idan har kasar ta gaza cimma ka’idar da EUDR ta gindaya mata daga nan zuwa watan Disambar 2025.

  • Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
  • Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Nijeriya dai, ta kasance ta hudu a duniya wajen nomansa; kana kuma, wadda take kan gaba wajen fitar da shi zuwa kasuwar duniya.

Akalla duk shekara, kananan manoma a kasar sun doshi 300,000 tare da noma tan 320,000, inda kuma fannin ke samar da riba; wadda ta kai kimanin dala miliyan 700.

Idan har Nijeriya ta gaza cimma wannan ka’ida ta EUDR, hakan zai iya jawo wa fannin gazawar fitar da shi zuwa Tarayyar Turai (EU).

LABARAI MASU NASABA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

An dai tsara ka’idar ta EUDR ne, domin a yi yaki da illolin muhalli da kuma sare itatuwa.

Yunkurin na daya daga cikin babban aikin yarjejeniyar EU, wadda kuma ta yi daidai da ka’idar ta Tarayyar Turan, musamman domin samar da dabarun bai wa Dazuka kariyar da ta kamata a daukacin fadin duniya baki-daya.

Kazalika, burin da EU ke son cimma shi ne, magance matsalar da Dazuka ke fuskanta tare kuma da tabbatar da ana bin diddigi wajen noman na Cocoa.

Majalisar Tarayyar Turai ta bayyana cewa, ta amince da ka’idar ta EUDR a 2022, wadda kuma ta fara aiki a ranar 29 ga watan Yunin 2023.

Sai dai, ka’idar ta fara aiki ne a ranar 30 ga watan Disambar 2024, wadda kuma cibiyoyin na EU suka daga wa’adin fara aikin ka’idar zuwa ranar 30 ga watan Disambar 2025.

Har ila yau, ka’idar ta bukaci daukacin Cocoa da ake nomawa da kuma jerin sauran amfanin gona, su zamo suna samun kariya tare kuma da tabbatar da an noma su bisa ka’ida.

Su ma kananan sana’oin hannu da matsakaitan sana’oi, akwai wa’adin da aka gindaya musu na su tabbatar da sun kai kayansu, wadanda aka taskance musu zuwa watan Yunin 2026, musamman domin su tabbaar da sun samar da ingantattun kaya.

Duba da cewa, kwana hudu ne kacal suka rage, gwamnatin tarayya ta umarci hukumominta da su tabbatar da sun tsara komai bisa ka’ida, domin kada a ki amincewa da Cocoa da za a fitar da shi zuwa kasuwannin Tarayyar Turan, musamman saboda yadda wasu manoma ke zuba masa sinadaran da ke wuci kima.

Bugu da kari, a ranar Litinin da ta gabata, gwamnatin ta yunkuro wajen karfafa matakan da suka dace na masana’ar Cocoa, domin dakile saba ka’idojin yin nomansa a kasar.

An gudanar da taron tattaunawa na kara jan hankali kan karfafa ka’idar ta EUDR ne a tsakanin Nijeriya da EU, a fadar shugaban kasa da ke Abuja, musamman domin a tabbatar da Nijeriya ta cimma wa’adin ranar da aka gindaya mata.

Dakta Kingsley Uzoma, Babban Mai Taimka Wa Shugaban Kasa a bangaren noma, domin samun riba da habaka fannin noma a jawabinsa a wajen tattaunawar ya sanar da cewa, Nijeriya a shirye take wajen cika ka’idar ta EUDR.

Uzoma ya bayyana cewa, manufar tattaunawar a kan batun ka’dar ta EUDR, wadda kuma ta haramta barin fitar da Cocoa da sauran amfanin gona da suke da illa zuwa kasuwar ta EU.

Ya ci gaba da cewa, fannin na noman Cocoa wani babban ginshike ne da ke kara habaka tattalin arzikin Nijeriya.

Daga 2023 zuwa 2024, Afirka ta noma Cocoa da ya kai kimanin tan miliyan 3.151, inda Nijeriya ta noma tan 320,000 tare da kuma bukatar kara fadada nomansa zuwa tan 500,000 a 2025, ta hanyar shirye-shiryen da ta kirkiro da su.

Bisa wasu alkaluman da Hukumar Kididdga ta Kasa (NBS) ta fitar sun nuna cewa; a zango na karshe na 2024, Nijeriya ta fitar da karin Cocoa da ya kai kimanin kashi 606, wanda ya kai na kusan Naira biliyan 171 a zango na karshe na 2023 zuwa Naira biliyan 1.2.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI
Noma Da Kiwo

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
Next Post
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

LABARAI MASU NASABA

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

October 30, 2025
Tinubu Ya Nada Musa Aliyu A Matsayin Shugaban ICPC

Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15

October 30, 2025
Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

October 30, 2025
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

October 30, 2025
Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

October 30, 2025
Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

October 30, 2025
Cocoa

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

October 30, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa

October 30, 2025
Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.