• English
  • Business News
Sunday, September 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?

by Rabi'u Ali Indabawa
4 hours ago
in Kasashen Ketare
0
Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan da kasashen Birtaniya da Canada da kuma Australia suka shiga jerin wadanda suka amince da kafuwar kasar Falasdinawa, ana sa rana wasu kasashen su ma su bi sahu.

To amma yaya kasashen Afirka ke kallon batun kafuwar kasar Falasdinawa?

  • Me Ya Sa Kamfanonin Jamus Fiye Da 560 Suka Zabi Wani Gari A Kasar Sin Don Gudanar Da Harkokinsu?
  • Matatar Dangote Ta Dawo Sayar Da Man Fetur A KuÉ—in Naira

Akasarin kasashen Afirka sun amince da kafuwar kasar Falasdinawa tun a shekarun 1980 bayan da bayan da jagoran Falasdinawa Yasser Arafat ya ayyana ‘‘yancin kan yankin a birnin Algiers.

Shugabanni irin su Thomas Sankara da Nelson Mandela duk sun alakanta fafutukar neman ‘‘yancin Falasdinawa da fafutikar kasashen Afirka na samun ‘‘yanci.

Sai dai, kasashe biyu – Kamaru da Eritrea – ba su yi hakan ba.

Labarai Masu Nasaba

Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa

An Cafke Bature ÆŠan Shekara 37 Kan Mutuwar ÆŠan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

 

Kamaru

Kasar Kamaru tana da alaka sosai da Isra’ila.

Daraktan fannin tsaro na Cibiyar Nazarin Tsaron Kasashen Afirka da tsare-tsare a Geneba, Dabid Otto ya ce Isra’ila na kallon Kamaru a matsayin daya daga cikin kawayenta na kusa a Afirka.

Ya ce “Kamaru ba za ta yi gangancin lalata alakar diflomasiyya da ke tsakaninta da Isra’ila ba.”

Ya ce alakarsu na da kwari sosai, kuma ya shafi batu ne na tsaro.

“Isra’ila ta taimaka sosai kuma tana ci gaba da taimakawa wajen kare gwamnatin Kamaru,” in ji shi.

Isra’ila ta bayar da horo, kuma ana da amannar cewa tana ci gaba da bai wa dakaru na musamman na Kamaru horo, wani abu da ke tabbatar da tsaron shugaban kasar.

“Haka nan kuma kyakkyawar alakar da ke tsakanin Kamru da Isra’ila ta sanya Kamaru din tana samun goyon baya daga Amurka ta bayan fage.”

Haka nan kuma matsayar Kamaru game da yankin Falasdinawa, akwai yiwuwar yana da alaka da artabun da take yi da ‘‘yan aware na yankin da aka fi amfani da harshen Turanci a kasar.

“Amincewa da kasar Falasdinawa zai iya haifar da karin matsi a cikin kasar, wanda hakan zai alamta cewa su ma masu fafutikar kwatar ‘yancin kai na kasar, su ma suna da hujja ke nan. Bayan kuwa Kamaru ta nanata cewa ita kasa daya ce wadda ba za ta balle ba,” in ji Otto.

A yancin lokaci Kamaru na kame bakinta ne kawai a duk lokacin da ake magana kan amincewa da kafa kasar Falasdinawa.

Ita kuwa Eritrea, tata matsayar na da dalilai da suka sha bamban, wadanda suka samo asali daga tata fafutikar ta samun ‘‘yanci.

 

Eritrea

A shekarar 1988 lokacin da Yasser Arafat ya ayyana ‘yancin kasar Falasdinawa, yana bukatar goyon bayan kasashen Afirka.

Daya daga cikin wadannan kasashen ita ce Ethiopia, wadda ita ce ke da mazaunin cibiyar Kungiyar Hadin kan Kasashen Afirka a wancan lokacin, wadda daga baya ta koma Tarayyar Afirka, a birnin Addis Ababa,” in ji mai sharhi kan siyasa dan kasar Ehiopia, Abdurahman Sayed.

“Gwamnatin mulkin soji ta wancan lokacin tana kuma goyon bayan Tarayyar Sobiet, saboda haka tana goyon bayan ‘‘yanci da kuma hakkin Falasdinawa.”

To amma a lokacin ita kuma Eritrea tana fafutikar neman ‘‘yancinta daga Habasha.

“A bayyane yake cewa a wancan lokacin Habasha ta mamaye Eritrea. Kuma a lokacin ‘‘yan Eritrea sun dauki makamai suna neman kwatar ‘‘yancin kansu daga Habasha,” in ji Sayed.

“A lokacin idan har Falasdinawa na son yin kyakkyawar alaka da Ethiopia to dole ne su nesanta kansu daga Eritrea, kuma ina ganin abin da Yasser Arafat ya yi ke nan, lamarin da bai yi wa ‘yan Eritrea dadi ba, ciki har da shugaban Eritrea na yanzu,” in ji shi.

Sai dai duk da haka, shugaban kasar Eritrea Isaias Afwerki ya nuna tausayawa ga Falasdinawa, a 2012 ma ya kada kuri’ar amincewa da bai wa yankin Falasdinawa matsayin “mai sa ido” a zauren Majalisar Dinkin Duniya.

Sai dai kuma ya yi watsi da tattaunawar zaman lafiya ta Oslo, wadda ta samar da tsarin zaman lafiya da ya bai wa Falasdinawa kwarya-kwaryar ‘‘yancin kai a wani yankin Gabar Yamma da Gaza, a matsayin wani mataki na samun ‘‘yancin kai.

“Shugaban Eritrea na daga cikin na farko-farko da suka yi watsi da yarjejeniyar Oslo a 1993, inda ya bayyana ta a matsayin maras amfani wadda ba za ta taimaka wajen warware rikicin da ake fama da shi ba ko kuma hankoron yankin na samun ‘‘yancin yankin Falasdinawa,” in ji Abdurahman Sayed.

Shugaba Afwerki ya ce ba ya goyon bayan kafa kasa biyu.

To sai dai zai iya fuskantar matsi daga cikin gida kasancewar kashi 55 cikin dari na al’ummar kasar Musulmai ne.

“Eritrea ta samu nasara a fafutukarta ta samun ‘‘yanci. Saboda haka a ce mutumin da ya jagoranci fafutikar samun ‘‘yanci kuma ba ya goyon bayan wasu su samu ‘‘yanci, za a ga kamar hakan ba abu ne mai kyau ba. Za su fuskanci matsi,” in ji Sayed.

BBC ta nemi jin ta-bakin gwamnatocin kasashen biyu, amma ba su bayar da amsa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Afrika
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Yusuf Ya Aike Da Sunayen Kwamishinoni Zuwa Majalisar Dokokin Jihar Kano

Next Post

Gwamna Yusuf Ya Samu KuÉ—aÉ—e A Cikin Wata 6 Fiye Da Yadda Na Samu A Cikin Shekaru 8 – Ganduje 

Related

Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa
Kasashen Ketare

Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa

7 days ago
An Cafke Bature ÆŠan Shekara 37 Kan Mutuwar ÆŠan Nijeriya Mazaunin Birtaniya
Kasashen Ketare

An Cafke Bature ÆŠan Shekara 37 Kan Mutuwar ÆŠan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

2 weeks ago
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Kasashen Ketare

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

3 weeks ago
Girgizar Ƙasa Ta Kashe Sama da Mutune 600 A Afghanistan
Kasashen Ketare

Girgizar Ƙasa Ta Kashe Sama da Mutune 600 A Afghanistan

4 weeks ago
Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi
Kasashen Ketare

Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi

1 month ago
Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida
Kasashen Ketare

Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

1 month ago
Next Post
Shari’a: Ganduje Ya Ki Na’am Da Tayin Jakadanci A Kasashen Afirka 

Gwamna Yusuf Ya Samu Kuɗaɗe A Cikin Wata 6 Fiye Da Yadda Na Samu A Cikin Shekaru 8 - Ganduje 

LABARAI MASU NASABA

Yaushe Mourinho Zai Koyar Da Kwallon Kafa A Kasashen Jamus Da Faransa?

Yaushe Mourinho Zai Koyar Da Kwallon Kafa A Kasashen Jamus Da Faransa?

September 28, 2025
Harin Bam: Gwamna Uba Sani Ya Kaddamar Da Sake Ginin Garin Tudun Biri 

Gwamnatin Kaduna Za Ta Horas Da ÆŠalibai 32,000 Sana’oin Hannu A Duk Shekara – Maiyaki

September 28, 2025
Shari’a: Ganduje Ya Ki Na’am Da Tayin Jakadanci A Kasashen Afirka 

Gwamna Yusuf Ya Samu KuÉ—aÉ—e A Cikin Wata 6 Fiye Da Yadda Na Samu A Cikin Shekaru 8 – Ganduje 

September 28, 2025
Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?

Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?

September 28, 2025
Kano

Gwamna Yusuf Ya Aike Da Sunayen Kwamishinoni Zuwa Majalisar Dokokin Jihar Kano

September 28, 2025
Yaushe Za Ta Kare Wa Haaland?

Yaushe Za Ta Kare Wa Haaland?

September 28, 2025
Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai

Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai

September 28, 2025
Abin Da Ya Sa Nijar Da Mali Da Burkina Faso Suka Fice Daga Kotun Duniya Ta ICC

Abin Da Ya Sa Nijar Da Mali Da Burkina Faso Suka Fice Daga Kotun Duniya Ta ICC

September 28, 2025
Daga Kallon Fina-finan Indiya Na Samu Sha’awar Fadawa Kannywood – Kamalu Mijinyawa

Daga Kallon Fina-finan Indiya Na Samu Sha’awar Fadawa Kannywood – Kamalu Mijinyawa

September 28, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Dawo Sayar Da Man Fetur A KuÉ—in Naira

September 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.