ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kashi 99.9 Cikin 100 Na ‘Yan Ta’adda A Arewacin Nijeriya ‘Yan Ƙasar Ne — Rahoto

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
1 month ago
'Yan ta'adda

Wani masanin tsaro da leken asiri, Yahuza Getso, ya bayyana cewa kashi 99 cikin 100 na dukkan ’yan bindiga da ke aiki a yankunan Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya ’yan Nijeriya ne.

 

Getso ya kuma jaddada cewa hukumomin tsaro sun san wadannan ’yan bindiga, sun san su da kuma inda suke.

ADVERTISEMENT
  • Allah Ya Tsarkake Iyalan Annabi (SAW) Daga Kazanta
  • Gwamnan Kano Ya Ɗauki Malaman Lissafi 400 Aiki

Masanin tsaron ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin wata hira da aka yi da shi a shirin Morning Brief na Channels Television.

 

LABARAI MASU NASABA

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

A cewarsa, “kashi 99.9 cikin 100 na ’yan bindigar da ke aiki a Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya ’yan Nijeriya ne. Mun san su, mun san su waye, mun san inda suke. Ba a wani boye suke ba ko a wani wuri mai wahalar isa.”

 

Ya yi wadannan bayani ne bayan sace dalibai 25 daga Sakandiren Gwamnati ta Maga, a Jihar Kebbi, da kuma kashe Birgediya Janar Musa Uba a Jihar Borno.

 

Jaridar LEADERSHIP ta tunatar da cewa harin makarantar ta Kebbi ya faru ne misalin karfe 4 na safiyar Litinin, lokacin da wasu ‘yan bindiga suka kutsa cikin makarantar, inda suka kashe mataimakin shugaban makarantar kuma suka sace dalibai mata 25.

 

Rahotanni sun nuna cewa mazauna yankin sun kasance cikin shirin ko-ta-kwana bayan samun bayanai na yiwuwar hare-hare a wasu kauyuka makwabtansu a ranar da ta gabata, amma hakan bai hana maharan kutsa yankin ba, lamarin da ya jefa al’umma cikin tsoro da alhini.

 

Haka kuma, Birgediya Janar Uba, wanda a farko Rundunar Sojin Nijeriya ta bayyana cewa yana cikin koshin lafiya bayan an yi masa kwanton-bauna da kungiyar ISWAP a kan hanyar Damboa–Biu a Jihar Borno, daga bisani an tabbatar da mutuwarsa.

 

Kungiyar ISWAP a ranar Talata ta saki hotuna da ke nuna ikirarin cewa ita ce ta kama kuma ta kashe babban jami’in.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace
Rahotonni

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

December 20, 2025
Tinubu Ya Nuna Kwarewa Da Gogewa A Sha’anin Mulkin Nijeriya – Bishir Dauda
Rahotonni

Tinubu Ya Nuna Kwarewa Da Gogewa A Sha’anin Mulkin Nijeriya – Bishir Dauda

December 19, 2025
Next Post
An Kammala Tsara Shawarwari 9,160 Da Aka Bayar A Babban Taro Na Uku Na Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin Ta 14

An Kammala Tsara Shawarwari 9,160 Da Aka Bayar A Babban Taro Na Uku Na Majalisar Wakilan Jama'ar Kasar Sin Ta 14

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.