ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Allah Ya Tsarkake Iyalan Annabi (SAW) Daga Kazanta

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani and Sulaiman
8 months ago
Annabi
A

ssalamu alaikum mabiyanmu masu albarka, kamar yadda muka saba duk mako mukan tsakuro wani batu na yabo da fifikon Annabi Muhammad SAW a kan sauran Annabawa da ma duk halittar Ubangiji baki daya, yau shafin na mu, zai yi tsokaci ne kan yadda Ubangiji tabaraka wata’ala, ya tsarkake iyalan Annabi SAW (Ahlul baiti) daga kazanta da aikata kowane irin sabo.

Annabi Ibrahim AS ya roki Ubangiji ya nesanta zuri’arsa daga bautar gunki wanda ake bautama wa, abun nufi wanda ake yanka jini ana bautar sa da nufin Ubangiji amma irin wanda yake fadar Annabi Sulaiman na sojoji ko ‘yan mazan jiya wannan ba gunki ba ne. Ya tabbata a Alkur’ani, mutanen Annabi Sulaiman suna kera masa gumaka na sojoji da tsoffin sarakuna ko kuma ‘yan mazan jiya, babu wanda ke zuwa gabansu da sunan bauta sai dai jinjina. Da wannan Malamai suke cewa, iyayen Annabi SAW suna kan addinin Annabi Ibrahim (Hanafiyya) kuma ya rokar wa zuri’arsa Ubangiji ya kare su daga bautar gunki kuma an amsa masa.

Amma ‘ya’yan gidan Manzon Allah SAW na cikin bargon nan (Annabi SAW, Sayyadina Ali, Sayyada Fatima, Hassan da Hussaini), ba wasu: A’li Akil, A’li Ja’afar, A’li Abbas ba; Allah ya kawar musu da kazanta (Giya, Caca, Bautar gunki, da Rantsuwa da kemaren tsafi), don haka, ‘ya’yan gidansa mai tsarki na cikin bargo komai za a yi, ba za su iya yin sabo ba. Tarihin Sayyadina Ali ya tabbatar da haka, duk yadda makiya suka yi don su tilasta shi ya yi sabo sai dai su gaji su bar shi, a karshe su ce “Allah ya yi gaskiya” suna nufin wannan Ayar. Haka Sayyada Fatima da ‘ya’yanta, ba za su iya yin sabo ba.

ADVERTISEMENT

A nan, za mu kara gane banbancin Annabi SAW da Annabi Ibrahim AS ba kusa suke ba. Ya roki daya an ba shi amma Annabi SAW, Allah bai fadi inda ya roka ba amma sai da aka ba shi abinda Annabi Ibrahim AS ya roka kuma aka hado shi da gara.

Annabi Ibrahim AS, da mutanensa suka kama shi za su sanya shi a wuta, wuridin da yake yi, shi ne “Hasbiyallah…” sai Allah ya sanya wutar ta zama lambu (aminci a gare shi), amma Annabi SAW, Ubangiji ne ya ce masa, “ya kai wannan Annabi, Allah ya isar maka – Ya Ayyuhan nabiyyu hasbukallah…”

LABARAI MASU NASABA

Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

A nan, za mu gane cewa, Annabi Ibrahim AS, shi ya yi wuridi amma Annabi SAW, Ubangiji ne ya yi masa wuridi da kansa.

Annabi Ibrahim AS, ya yi Hijira zuwa garin da ake bautar Ubangiji, misali mu ce, daga Yamen zuwa Falasdinu inda Kur’ani ya ke cewa, “Inni Muhajirun ila rabbi sayahdin – ni na yi hijra zuwa ga Ubangiji na, zai shiryar da ni.” Amma Annabi SAW tafiyar da shi aka yi. Da fadinsa “Subhanallazi asra bi abdihi… – tsarki ya tabbata ga wanda ya tafiyar da bawansa …”

A nan, za mu gane cewa, Annabi Ibrahim AS, shi yake tuka kansa, amma Annabi SAW, shi Ubangiji ne ya tuka shi.

A wani wuri kuma da Ubangiji ya tattaro duka Manzonninsa, da fadinsa “Tilkarrusulu faddalna ba’dahum ala ba’ad – wadan can Annabawan, mun fifita wasu akan wasu”. Amma “Warafa’a ba’dahum darajat – wasu mun daga darajarsu akan wasu”.

A nan, za mu iya fahimtar cewa, duk Ubangiji ya fifita Manzonninsa akan wasu, amma ya nuna cewa ya daga darajar Annabi SAW a kan dukkansu.

In mun dauka kirarin da Ubangiji ya yi wa Annabi Musa AS da fadinsa “wakallamallahu Musa taklima – Ubangiji ya yi maganganu da Annabi Musa”, Annabi Musa shi yake zuwa da kansa inda Ubangiji ke ganawa da shi amma Annabi SAW, inda aka gana da shi, a saman sama, (Dana Fatadalla, fakana kaba kausaini au adna, fa’auha ila abdihi ma’auha), a lokacin an riga an shige Jibrilu, sannan duk aka yi wannan tafiyoyi – Dana Fatadalla, har ya zama kamar kausani ko kuma mafi kusa da haka ma. Wadanda ke fassarawa da cewa, (fa’auha ila abdihi ma’auha), Mala’ika Jibrilu ne ya yi wa bawansa Annabi Muhammad SAW wahayi, lallai kafarsu ta zame, ya dace a yi gyara. Da yawa a Tafsiri, Shehu Ibrahim Inyass Kaulaha zai ce, Mai tafsiri Jalal Arabi ya ce anan, amma fa kafarsa ta zame, ba haka abun yake ba!

A nan gabar ne, Shehu Ibrahim Inyass ke sharhi da cewa, “fa’auha ila abdihi ma’auha”, kalmar “ma” itace a ayar (wayakluku “ma” la ta’alamun), da ita ake halartar komai.

A nan, za mu gane cewa, Ubangiji ya yi magana da Annabi Musa ta shamaki amma da zai yi magana da Annabi SAW, gaba-da-gaba aka yi. Ubangiji ya fada mana cewa, Annabi Musa AS ya nemi ya ga Ubangiji amma bai amsa masa ba, amma ya gaya mana cewa, (ma kazabal fu’adu ma ra’a – zuciyar Annabi SAW  ba ta karyata abinda idonta ya gani ba), kuma ya ruwaito mana abinda ya faru da Annabi Musa AS lokacin da aka tambaye shi, (Menene a hannunka ya Annabi Musa?) Duk abinda ya faru tsakanin Ubangiji da Annabi Musa AS, sai da Ubangiji ya ba mu labarin komai  amma a yayin zantawarsa da Annabi SAW, sai dai kawai aka ji ya ce, (fa auha ila abdihi ma’auha – sai ya yi wahayi ga bawansa) babu wani cikin halitta da ya isa yasan me aka yi masa wahayi! Don a samu saukin wannan ayar, wasu malamai suka ce, Ubangiji ya yi wa bawansa wahayin komai, ma’ana ya sanar da shi komai.

Yana daga cikin abinda Fakrurrazi ya bayyana a Tafsirin ayar (Tilkarrusulu…), duka al’ummar Musulmi sun hadu cewa, ubangiji ya daga darajar wasu Annabawa akan wasu, wani Annabi yafi wani Annabi, amma Annabi SAW in aka hade dukkansu, ya fi su, in aka yi gogayya daya bayan daya, ya fi kowa, saboda irin aikinsa ba kamar na su ba.

 

Za mu iya gane hakan ta fuskoki kamar haka:

1 – An aiko Annabi SAW don ya zama rahama ga duk halitta (wama arsalnaka, illa rahmatan lil alamin) amma kowanne Annabi, rahama ne ga duk iya kauyensa (mutanensa), iya kacin wadanda suka yi imani da shi, sauran kuwa, sai ya ce duk a jefa su a wuta. Uwa uba Shari’ar Annabi Musa, me cewa, idan kun hadu da Larabawa ko Farisawa, ku kira su zuwa ga Addininku, idan sun bi, su zama bayinku, idan sun ki, ku kashe su gaba daya (Mata da Maza, yara) kuma sun ce wai Allah ne ya fadi haka. Ubangiji ba zai fadi haka ba. Don haka, suke kashe Falasdinawa, domin su a wurinsu ibada suke yi.

Don haka, fifikon Annabi SAW akan sauran Annabawa a fili yake. An aiko shi ga duk duniya, su kuma ga mutanen kauyensu kawai. Kuma shi yasa, Annabi SAW ya zama mafi rahamar halitta, don ba za a samu wani a saman shi ba. Tunda ya zama rahama ga duk halitta, to ya zama shugaban halitta.

Annabi SAW ya ce, hannun da ya bayar, ya fi hannun da ya amsa.

… Za mu ci gaba daga (2) a mako mai zuwa.

Alhamdulillah… irin wannan karatu da zai nuna maka daraja da soyayya ta Annabi SAW, shi al’ummar Annabi SAW ke bukata ba wanda zai koya maka cin fuska ga reshi da iyalan gidansa ba.

Annabi
Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
+ posts Bio
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Falalar Haɗa Basmala da Suratul Fatiha
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Falalar Neman Tsari Daga Sharrin Shaidan
Annabi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje
Dausayin Musulunci

Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

July 3, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)
Dausayin Musulunci

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Manzon Allah
Dausayin Musulunci

Falalar Haɗa Basmala da Suratul Fatiha

June 19, 2026
Next Post
Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Ƙaddamar Da Jakadun Wayar Da Kai Game Da Rigakafi

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Ƙaddamar Da Jakadun Wayar Da Kai Game Da Rigakafi

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.