ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kashi 99.9 Cikin 100 Na ‘Yan Ta’adda A Arewacin Nijeriya ‘Yan Ƙasar Ne — Rahoto

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
7 months ago
'Yan ta'adda

Wani masanin tsaro da leken asiri, Yahuza Getso, ya bayyana cewa kashi 99 cikin 100 na dukkan ’yan bindiga da ke aiki a yankunan Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya ’yan Nijeriya ne.

 

Getso ya kuma jaddada cewa hukumomin tsaro sun san wadannan ’yan bindiga, sun san su da kuma inda suke.

ADVERTISEMENT
  • Allah Ya Tsarkake Iyalan Annabi (SAW) Daga Kazanta
  • Gwamnan Kano Ya Ɗauki Malaman Lissafi 400 Aiki

Masanin tsaron ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin wata hira da aka yi da shi a shirin Morning Brief na Channels Television.

 

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

A cewarsa, “kashi 99.9 cikin 100 na ’yan bindigar da ke aiki a Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya ’yan Nijeriya ne. Mun san su, mun san su waye, mun san inda suke. Ba a wani boye suke ba ko a wani wuri mai wahalar isa.”

 

Ya yi wadannan bayani ne bayan sace dalibai 25 daga Sakandiren Gwamnati ta Maga, a Jihar Kebbi, da kuma kashe Birgediya Janar Musa Uba a Jihar Borno.

 

Jaridar LEADERSHIP ta tunatar da cewa harin makarantar ta Kebbi ya faru ne misalin karfe 4 na safiyar Litinin, lokacin da wasu ‘yan bindiga suka kutsa cikin makarantar, inda suka kashe mataimakin shugaban makarantar kuma suka sace dalibai mata 25.

 

Rahotanni sun nuna cewa mazauna yankin sun kasance cikin shirin ko-ta-kwana bayan samun bayanai na yiwuwar hare-hare a wasu kauyuka makwabtansu a ranar da ta gabata, amma hakan bai hana maharan kutsa yankin ba, lamarin da ya jefa al’umma cikin tsoro da alhini.

 

Haka kuma, Birgediya Janar Uba, wanda a farko Rundunar Sojin Nijeriya ta bayyana cewa yana cikin koshin lafiya bayan an yi masa kwanton-bauna da kungiyar ISWAP a kan hanyar Damboa–Biu a Jihar Borno, daga bisani an tabbatar da mutuwarsa.

 

Kungiyar ISWAP a ranar Talata ta saki hotuna da ke nuna ikirarin cewa ita ce ta kama kuma ta kashe babban jami’in.

'Yan ta'adda
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
'Yan ta'adda
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

'Yan ta'adda
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
'Yan ta'adda
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
An Kammala Tsara Shawarwari 9,160 Da Aka Bayar A Babban Taro Na Uku Na Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin Ta 14

An Kammala Tsara Shawarwari 9,160 Da Aka Bayar A Babban Taro Na Uku Na Majalisar Wakilan Jama'ar Kasar Sin Ta 14

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.