• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Bi Diddigin Yadda Aka Kai Harin Gidan Yarin — Majalisar Wakilai

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Za Mu Bi Diddigin Yadda Aka Kai Harin Gidan Yarin — Majalisar Wakilai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Wakilai ta sha alwashin bankado yadda aka fasa gidan yarin kuje a ranar 5 ga watan Yuli, wanda aka danganta harin da kungiyar ‘yan ta’adda ta ISWAP.

Shugaban Kwamitin Tsaro da Bayanan Sirri na Majalisar Wakilai, Sha’aban Sharada, ne ya bayyana hakan yayin zaman bincike tare da jin ba’asi game da harin da ‘yan ta’adda suka kai a gidan yarin na Kuje da ke Abuja.

  • Miyetti Allah Ta Roki Soludo Ka Da Ya Soke Kiwon Shanu A Jiharsa
  • Kotu Ta Bai Wa Kwamishinan Gona Wa’adin Kwana 2 Ya Dawo Da Tirakta 58 Da Ya Sayar A Zamfara

Tun a ranar 22 ga watan Yuli ne dai Majalisar Wakilai ta kafa kwamitin hadin gwiwa kan tsaro da binciken sirri da kwamitoci masu alaka da tsaro don bincikar musabbabin harin da aka kai wa gidan yarin na Kuje.

Sharada, wanda shi ne shugaban kwamitin hadin gwiwar, ya tabbatar wa jama’a cewa mambobin kwamitin ba za su bar lamarin ya wuce haka kawai sakaka ba ba tare da daukar matakan da suka dace ba.

Ya ce majalisar za ta binciki lamarin da ya haddasa faruwar lamarin, inda ya ce za a yi kokari matuka don tabbatar da samar da tsaro a cikin ginin gidan gyaran halin da kewayensa.

Labarai Masu Nasaba

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

Ya ce, za a samar da matakan da za a kiyaye sake afkuwar lamarin a nan gaba da sauran sassan kasar nan.

Ya ce, majalisar za ta kuma tabbatar da bin diddigin matakan da za a bi don kare rayuka da dukiyoyin mazauna babban birnin tarayya, Abuja da na daukacin Nijeriya.

Ya kuma tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa kwamitin hadin guiwar zai yi tsayin daka don aiwatar da aikin da aka dora masa alhaki.

Ya ce an samu bayanai masu ma’ana daga manyan daraktocin ma’aikatar harkokin gwamnati da hukumar leken asiri ta kasa da sauran hukumomi da ke bada bayanai ga hukumomin tsaro a Nijeriya.

Kwamitin, ya ce zai sake gayyatar shugabannin tsaro da sauran shugabannin hukumomin tsaro ciki har da wasu ministocin da suka kasa amsa gayyatar da aka yi musu a baya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BincikeGidan Yarin KujeHariISWAPMajalisar Wakilai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Miyetti Allah Ta Roki Soludo Ka Da Ya Soke Kiwon Shanu A Jiharsa

Next Post

Zamu Ci Gaba Da Yajin Aiki Har Sai Bukatunmu Sun Biya – ASUU

Related

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

13 hours ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

20 hours ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

22 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

23 hours ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

1 day ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

1 day ago
Next Post
Zamu Ci Gaba Da Yajin Aiki Har Sai Bukatunmu Sun Biya – ASUU

Zamu Ci Gaba Da Yajin Aiki Har Sai Bukatunmu Sun Biya - ASUU

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.