ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Bi Diddigin Yadda Aka Kai Harin Gidan Yarin — Majalisar Wakilai

by Sadiq
4 years ago
Diddigi

Majalisar Wakilai ta sha alwashin bankado yadda aka fasa gidan yarin kuje a ranar 5 ga watan Yuli, wanda aka danganta harin da kungiyar ‘yan ta’adda ta ISWAP.

Shugaban Kwamitin Tsaro da Bayanan Sirri na Majalisar Wakilai, Sha’aban Sharada, ne ya bayyana hakan yayin zaman bincike tare da jin ba’asi game da harin da ‘yan ta’adda suka kai a gidan yarin na Kuje da ke Abuja.

  • Miyetti Allah Ta Roki Soludo Ka Da Ya Soke Kiwon Shanu A Jiharsa
  • Kotu Ta Bai Wa Kwamishinan Gona Wa’adin Kwana 2 Ya Dawo Da Tirakta 58 Da Ya Sayar A Zamfara

Tun a ranar 22 ga watan Yuli ne dai Majalisar Wakilai ta kafa kwamitin hadin gwiwa kan tsaro da binciken sirri da kwamitoci masu alaka da tsaro don bincikar musabbabin harin da aka kai wa gidan yarin na Kuje.

ADVERTISEMENT

Sharada, wanda shi ne shugaban kwamitin hadin gwiwar, ya tabbatar wa jama’a cewa mambobin kwamitin ba za su bar lamarin ya wuce haka kawai sakaka ba ba tare da daukar matakan da suka dace ba.

Ya ce majalisar za ta binciki lamarin da ya haddasa faruwar lamarin, inda ya ce za a yi kokari matuka don tabbatar da samar da tsaro a cikin ginin gidan gyaran halin da kewayensa.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Ya ce, za a samar da matakan da za a kiyaye sake afkuwar lamarin a nan gaba da sauran sassan kasar nan.

Ya ce, majalisar za ta kuma tabbatar da bin diddigin matakan da za a bi don kare rayuka da dukiyoyin mazauna babban birnin tarayya, Abuja da na daukacin Nijeriya.

Ya kuma tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa kwamitin hadin guiwar zai yi tsayin daka don aiwatar da aikin da aka dora masa alhaki.

Ya ce an samu bayanai masu ma’ana daga manyan daraktocin ma’aikatar harkokin gwamnati da hukumar leken asiri ta kasa da sauran hukumomi da ke bada bayanai ga hukumomin tsaro a Nijeriya.

Kwamitin, ya ce zai sake gayyatar shugabannin tsaro da sauran shugabannin hukumomin tsaro ciki har da wasu ministocin da suka kasa amsa gayyatar da aka yi musu a baya.

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Zamu Ci Gaba Da Yajin Aiki Har Sai Bukatunmu Sun Biya – ASUU

Zamu Ci Gaba Da Yajin Aiki Har Sai Bukatunmu Sun Biya - ASUU

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.