ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Bi Diddigin Yadda Aka Kai Harin Gidan Yarin — Majalisar Wakilai

by Sadiq
4 years ago
Diddigi

Majalisar Wakilai ta sha alwashin bankado yadda aka fasa gidan yarin kuje a ranar 5 ga watan Yuli, wanda aka danganta harin da kungiyar ‘yan ta’adda ta ISWAP.

Shugaban Kwamitin Tsaro da Bayanan Sirri na Majalisar Wakilai, Sha’aban Sharada, ne ya bayyana hakan yayin zaman bincike tare da jin ba’asi game da harin da ‘yan ta’adda suka kai a gidan yarin na Kuje da ke Abuja.

  • Miyetti Allah Ta Roki Soludo Ka Da Ya Soke Kiwon Shanu A Jiharsa
  • Kotu Ta Bai Wa Kwamishinan Gona Wa’adin Kwana 2 Ya Dawo Da Tirakta 58 Da Ya Sayar A Zamfara

Tun a ranar 22 ga watan Yuli ne dai Majalisar Wakilai ta kafa kwamitin hadin gwiwa kan tsaro da binciken sirri da kwamitoci masu alaka da tsaro don bincikar musabbabin harin da aka kai wa gidan yarin na Kuje.

ADVERTISEMENT

Sharada, wanda shi ne shugaban kwamitin hadin gwiwar, ya tabbatar wa jama’a cewa mambobin kwamitin ba za su bar lamarin ya wuce haka kawai sakaka ba ba tare da daukar matakan da suka dace ba.

Ya ce majalisar za ta binciki lamarin da ya haddasa faruwar lamarin, inda ya ce za a yi kokari matuka don tabbatar da samar da tsaro a cikin ginin gidan gyaran halin da kewayensa.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ya ce, za a samar da matakan da za a kiyaye sake afkuwar lamarin a nan gaba da sauran sassan kasar nan.

Ya ce, majalisar za ta kuma tabbatar da bin diddigin matakan da za a bi don kare rayuka da dukiyoyin mazauna babban birnin tarayya, Abuja da na daukacin Nijeriya.

Ya kuma tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa kwamitin hadin guiwar zai yi tsayin daka don aiwatar da aikin da aka dora masa alhaki.

Ya ce an samu bayanai masu ma’ana daga manyan daraktocin ma’aikatar harkokin gwamnati da hukumar leken asiri ta kasa da sauran hukumomi da ke bada bayanai ga hukumomin tsaro a Nijeriya.

Kwamitin, ya ce zai sake gayyatar shugabannin tsaro da sauran shugabannin hukumomin tsaro ciki har da wasu ministocin da suka kasa amsa gayyatar da aka yi musu a baya.

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Zamu Ci Gaba Da Yajin Aiki Har Sai Bukatunmu Sun Biya – ASUU

Zamu Ci Gaba Da Yajin Aiki Har Sai Bukatunmu Sun Biya - ASUU

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.