ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hatsarin Tankar Mai Da Gobara Sun Yi  Ajalin Mutum 3 A Kano

by Abubakar Sulaiman
3 weeks ago
Gobara

Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano ta tabbatar da mutuwar mutane uku a sakamakon hatsarin mota mai ɗauke da man fetur da kuma gobarar wani gini daban, duka a ranar Juma’a.

A cewar sanarwar ACFO Saminu Yusif Abdullahi, hatsarin farko ya faru ne da misalin ƙarfe 1:30 na rana a kan titin Zariya kusa da Kasuwar Kura. Tankar mai ɗauke da kimanin lita 30,000 ta kife ta kama da wuta, inda direban ya buge wani mai keke amma ya tsira, sai dai mutane ukun da aka tarar a sume daga baya an tabbatar da mutuwarsu.

  • Yadda Gobara Ta Lashe Kasuwar Katako Ta Gwambe
  • Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Hukumar ta ce jami’anta tare da haɗin gwuiwar ƴansanda da hukumar kiyaye haɗurra sun yi nasarar kashe gobarar da ceto mutane, sannan suka miƙa gawarwakin ga ASP Ahmad Lawan na Ofishin ƴansanda na Kura. Motoci biyu na kashe gobara daga shalƙwatar ofishin Kura ne suka yi aikin ceton. A halin yanzu ana ci gaba da bincike don gano musabbabin hatsarin.

ADVERTISEMENT

Kimanin da ƙarfe 2:45 na rana, an sake samun gobara a wani ginin kasuwanci bene biyu a Hamisu Plaza, unguwar Tarauni, a kan titin Maiduguri. Sanarwar ta bayyana cewa shaguna uku ne gobarar ta shafa kai tsaye, yayin da sauran shagunan na ƙasa aka yi nasarar kare su. Motar kashe gobara daga filin bikin baje koli (Trade Fair) ta taimaka wajen kashe wutar, kuma har yanzu babu cikakken bayani kan abin da ya jawo gobarar.

Daraktan Hukumar Kashe Gobara ta jihar, Alhaji Sani Anas, ya shawarci jama’a su kula da yadda suke amfani da wuta musamman a lokacin hunturu, tare da yin kira ga direbobi da su yi taka-tsantsan a hanya. Ya ce bin ƙa’idojin tuki da guje wa sakaci na iya hana aukuwar manyan haɗurra da ke janyo hasarar rayuka da dukiyoyi.

LABARAI MASU NASABA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Uku Bayan Rufe Makarantu A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.