ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861 Na 2026 Ga Majalisar Dokokin Jihar Zamfara

by Sulaiman and Hussein Yero
2 weeks ago
Gwamna lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gabatar da ƙudirin kasafin kuɗi na shekarar 2026 mai darajar Naira Biliyan 861 ga Majalisar Dokokin Jihar, inda ya bayyana shi a matsayin taswirar sauyi da kuma shaida cewa Zamfara na kan hanyarta ta tashi tsaye da ƙarfi.

 

An gabatar da kasafin ne a ranar Alhamis a birnin Gusau.

ADVERTISEMENT
  • Duniya Za Ta Kara Kyau In Ba A Nuna Fin Karfi
  • Ma’aikatan Shari’a Sun Fara Yajin Aiki Kan Bashin Albashi Da Kuɗin Hutu A Kogi

A cikin sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, an bayyana cewa kasafin kuɗin ya ware Naira Biliyan 714, wato kashi 83 cikin 100, domin ayyukan raya ƙasa, yayin da aka ware Naira Biliyan 147.279 domin ayyukan yau da kullum na gwamnati, wanda ya kai kashi 17 cikin 100.

 

LABARAI MASU NASABA

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sanarwar ta ƙara da cewa, an tanadi Naira Biliyan 65 domin ilimi, Naira Biliyan 87 domin kiwon lafiyar al’umma, Naira Biliyan 86 a bangaren noma, Naira Biliyan 45 domin tabbatar da tsaro da zaman lafiya, Naira Biliyan 22 domin kare muhalli, sai Naira Biliyan 17 domin jin daɗin al’umma da tallafa musu.

 

A jawabinsa gaban majalisar, Gwamna Lawal ya ce gwamnatinsa, wadda aka zaba bisa alƙawarin ceto, gyara da farfaɗo da jihar, ta yi aiki tuƙuru wajen dawo da amincewa ga hukumomin gwamnati, gina manyan sassa, da shimfiɗa tubalin ci gaba mai ɗorewa.

 

Ya ce, mutanen Zamfara da a baya suka shiga damuwa sakamakon sakaci, yanzu sun fara ganin hasken gaskiya, ci gaba da sabon alƙibla.

 

Ya bayyana kasafin 2026 a matsayin sabon babi a wannan tafiya ta sauyi, yana mai cewa ba tsari ne na kuɗi kawai ba, illa allawari ne na siyasa da nufin tabbatar da zaman lafiya da kuma hanzarta bunƙasar da al’umma ke muradi.

 

A cewarsa, kasafin an tsara shi ne domin samun ribar tsare-tsaren shirin ceto na matakai shida da gwamnatinsa ke aiwatarwa, waɗanda suka haɗa da ƙarfafa tsaro, sabunta noma domin samar da wadatar abinci, inganta tsarin kiwon lafiya a kowane yanki, faɗaɗa damar samun nagartaccen ilimi, hanzarta raya ababen more rayuwa, da kuma ƙarfafa matasa, mata da masu rauni.

 

Gwamnan ya jaddada cewa kashi 17 na kuɗaɗen da aka ware domin kashe-kashen yau da kullum na nuna tsauraran matakan kula da kuɗi da kuma nagartar tafiyar da al’amuran gwamnati.

 

Ya ce, a ma’aunin ƙasa da kasa, ana ba da shawarar kada irin wannan kashe-kashe ya haura kashi 60, alhali Zamfara ta tsaya nesa da hakan, lamarin da ke nuna kyakyawan yanayin tafiyar da kuɗaɗe bisa ƙa’ida.

 

Ya kuma bayyana cewa, ginshiƙin kasafin shi ne ɓangaren ayyukan raya kasa da aka ware kashi 83, wanda ya kira tarihi, domin gina manyan ayyuka, karfafa tsaro, farfaɗo da noma, da kuma samar wa matasa damarmaki.

 

Gwamna Lawal ya ce, babu wani buri da za a cimma, daga tsaro zuwa ilimi, daga noma zuwa gine-gine, daga gyaran ma’aikata zuwa farfaɗo da tattalin arziki, face da cikakken goyon bayan siyasa, jajircewar gwamnati, da haɗa kai da majalisar dokoki.

 

A ƙarshe, ya miƙa kasafin kuɗi mai taken “Kasafin Tabbataccen Zaman Lafiya da Ci Gaba” na Naira biliyan 861.337 domin nazari da amincewa, yana mai cewa wannan kasafi yarjejeniya ce da al’umma, taswirar sauyi da kuma sanarwar cewa Zamfara za ta tashi tsaye da ƙarfi fiye da da.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa
Labarai

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli
Labarai

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Next Post
Peng Liyuan Da Brigitte Macron Sun Ziyarci Gidan Wasannin Kwaikwayo Ta Al’umma Ta Beijing

Peng Liyuan Da Brigitte Macron Sun Ziyarci Gidan Wasannin Kwaikwayo Ta Al’umma Ta Beijing

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.