ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duniya Za Ta Kara Kyau In Ba A Nuna Fin Karfi

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Duniya

Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya sanar a kwanan baya cewa, ba zai gayyaci Afirka ta Kudu ta halarci taron kolin kungiyar G20 da za a gudanar a birnin Miami na kasar Amurka a shekara mai zuwa ba.

Kasancewarsa muhimmin dandali na hadin gwiwar tattalin arzikin duniya, wakilci da hakuri su ne tushen kungiyar G20. Daga cikin kasashe mambobin kungiyar G20, kungiyar tarayyar Afirka (AU) da kuma kasar Afirka ta kudu, su biyu ne kadai suka fito daga nahiyar Afirka. Don haka, ba kawai kasar Afirka ta Kudu na wakiltar kanta ba ce, har ma tana dauke da nauyin fitar da muryar kasashen nahiyar game da gudanar harkokin tattalin arzikin duniya. Amma sai ga shi Amurka ta sanya bukatarta sama da matsayar sassan kasa da kasa, tana mai daukar odar duniya a matsayin wadda za ta iya takewa, tare da kallon hukumomin kasa da kasa a matsayin dan wasan dara da za ta iya sauyawa wuri a duk lokacin da take so, wanda hakan ya shaida yadda Amurka ke nuna fin karfi a duniya, da ma matsalar da ake fuskanta a tsarin kula da al’amuran duniya.

  • Ma’aikatan Shari’a Sun Fara Yajin Aiki Kan Bashin Albashi Da Kuɗin Hutu A Kogi
  • Ko Kwalliya Za Ta Biya Kuɗin Sabulu Kan Sauye-sauyen Tinubu Na Inganta Tsaro A Nijeriya?

Amma irin yanayi na nuna fin karfi da Amurka ke yi ba zai dore ba, ta la’akari da jerin wasu muhimman tarukan da aka gudanar a watan Nuwamban da ya gabata, wadanda suka samu muhimman nasarori ko da yake ba tare da hallarar kasar Amurka ba.

ADVERTISEMENT

A ranar 7 ga watan Nuwamban da ya gabata, hukumar kula da hakkin bil Adam ta MDD ta kira taron musamman, don yin nazari a kan harkokin hakkin bil Adam na kasar Amurka a karo na hudu. Tsarin nazarin harkokin hakkin dan Adam na kasa da kasa muhimmin tsari ne da MDD ta kafa don neman inganta musaya da hadin gwiwa a tsakanin kasa da kasa ta fannin kare hakkin dan Adam. Tun kafuwarsa a shekarar 2007, an gudanar da nazarin a kan kasashe mambobi 193 na MDD har sau uku, amma Amurka ta ki a yi mata sabon zagaye na nazarin. Duk da haka, sassan kasa da kasa sun tabbatar da gudanar tsarin nazarin ba tare da tsayawa ba, ta hanyar tsara sabon jadawali, da kuma gabatar da sabbin shawarwari, ta yadda tsarin kula da hakkin dan Adam na duniya zai kara kare adalci da samar da tasiri mai muhimmanci.

Haka nan kuma a ranar 10 ga watan Nuwamban, an gudanar da taron masu sa hannu a yarjejeniyar sauyin yanayi ta MDD (COP30) a birnin Belém na kasar Brazil. Amurka a matsayinta na kasar da ta fi yawan fitar da hayaki mai dumama yanayi a tarihi, ba ta tura wakilai masu babban matsayi zuwa taron ba, ban da wani mai taimakawa sakataren harkokin wajen kasar da ke kula da harkokin muhalli. Sai dai hakan bai haifar da cikas ga taron ba, bisa shawarwarin da mahalarta taron suka shafe tsawon kwanaki 13 suna yi, taron ya zartas da shawara mai taken “kira ga duniya: hadin gwiwa don tinkarar sauyin yanayi”, shawarar da ta bukaci kasashe masu ci gaba su taimaka wa kasashe masu fama da koma baya, wajen inganta kwarewarsu ta fannin tinkarar sauyin yanayi.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Ya zuwa ranar 22 ga watan Nuwamban, an kaddamar da taron kolin G20 a birnin Johannesburg na kasar Afirka ta Kudu, taron da ya kasance irinsa na farko da aka gudanar a nahiyar Afirka. Amma gwamnatin kasar Amurka ba ta halarci taron ba, har ma ta yi ta yi wa kasar Afirka ta Kudu mai masauki baki matsin lamba tun ba a fara taron ba, ta kuma ki yarda da taron ya bayar da sanarwa bisa taken daidaiton kungiyar G20 ba tare da samun amincewarta ba. Duk da hakan, mahalarta taron sun cimma daidaito a ranar farko da aka bude taron, har ma suka zartas da “sanarwar Johannesburg ta shugabannin G20” wadda ke kunshe da tanade-tanade 122, wanda hakan ya kafa sabon tarihin G20.

Lallai jerin abubuwa da suka wakana sun shaida yadda al’ummomin duniya ke rungumar hadin gwiwar cin moriyar juna a maimakon nuna fin karfi da ra’ayi na kashin kai. Zamanin da komai sai ya samu amincewar Amurka yana dab da karewa, kuma ana fitowa da sabon tsarin da kasa da kasa ke binsa a hadin gwiwarsu, yayin da suke kula da harkokin duniya. Yadda Amurka ke kauracewa tarukan bai haifar da komai ba, illa yin watsi da ita a fannin kulawa da harkokin duniya. Harkokin duniya na gudana yadda ya kamata, ko ba tare da Amurka ta sa hannu a ciki ba, kuma duniya za ta kara kyau in ba a nuna fin karfi.

 

 

 

Duniya
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya
Duniya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Kama 'Yan Ta'adda 74, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace 318 A Watan Nuwamba 

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.