ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duniya Za Ta Kara Kyau In Ba A Nuna Fin Karfi

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
Duniya

Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya sanar a kwanan baya cewa, ba zai gayyaci Afirka ta Kudu ta halarci taron kolin kungiyar G20 da za a gudanar a birnin Miami na kasar Amurka a shekara mai zuwa ba.

Kasancewarsa muhimmin dandali na hadin gwiwar tattalin arzikin duniya, wakilci da hakuri su ne tushen kungiyar G20. Daga cikin kasashe mambobin kungiyar G20, kungiyar tarayyar Afirka (AU) da kuma kasar Afirka ta kudu, su biyu ne kadai suka fito daga nahiyar Afirka. Don haka, ba kawai kasar Afirka ta Kudu na wakiltar kanta ba ce, har ma tana dauke da nauyin fitar da muryar kasashen nahiyar game da gudanar harkokin tattalin arzikin duniya. Amma sai ga shi Amurka ta sanya bukatarta sama da matsayar sassan kasa da kasa, tana mai daukar odar duniya a matsayin wadda za ta iya takewa, tare da kallon hukumomin kasa da kasa a matsayin dan wasan dara da za ta iya sauyawa wuri a duk lokacin da take so, wanda hakan ya shaida yadda Amurka ke nuna fin karfi a duniya, da ma matsalar da ake fuskanta a tsarin kula da al’amuran duniya.

  • Ma’aikatan Shari’a Sun Fara Yajin Aiki Kan Bashin Albashi Da Kuɗin Hutu A Kogi
  • Ko Kwalliya Za Ta Biya Kuɗin Sabulu Kan Sauye-sauyen Tinubu Na Inganta Tsaro A Nijeriya?

Amma irin yanayi na nuna fin karfi da Amurka ke yi ba zai dore ba, ta la’akari da jerin wasu muhimman tarukan da aka gudanar a watan Nuwamban da ya gabata, wadanda suka samu muhimman nasarori ko da yake ba tare da hallarar kasar Amurka ba.

ADVERTISEMENT

A ranar 7 ga watan Nuwamban da ya gabata, hukumar kula da hakkin bil Adam ta MDD ta kira taron musamman, don yin nazari a kan harkokin hakkin bil Adam na kasar Amurka a karo na hudu. Tsarin nazarin harkokin hakkin dan Adam na kasa da kasa muhimmin tsari ne da MDD ta kafa don neman inganta musaya da hadin gwiwa a tsakanin kasa da kasa ta fannin kare hakkin dan Adam. Tun kafuwarsa a shekarar 2007, an gudanar da nazarin a kan kasashe mambobi 193 na MDD har sau uku, amma Amurka ta ki a yi mata sabon zagaye na nazarin. Duk da haka, sassan kasa da kasa sun tabbatar da gudanar tsarin nazarin ba tare da tsayawa ba, ta hanyar tsara sabon jadawali, da kuma gabatar da sabbin shawarwari, ta yadda tsarin kula da hakkin dan Adam na duniya zai kara kare adalci da samar da tasiri mai muhimmanci.

Haka nan kuma a ranar 10 ga watan Nuwamban, an gudanar da taron masu sa hannu a yarjejeniyar sauyin yanayi ta MDD (COP30) a birnin Belém na kasar Brazil. Amurka a matsayinta na kasar da ta fi yawan fitar da hayaki mai dumama yanayi a tarihi, ba ta tura wakilai masu babban matsayi zuwa taron ba, ban da wani mai taimakawa sakataren harkokin wajen kasar da ke kula da harkokin muhalli. Sai dai hakan bai haifar da cikas ga taron ba, bisa shawarwarin da mahalarta taron suka shafe tsawon kwanaki 13 suna yi, taron ya zartas da shawara mai taken “kira ga duniya: hadin gwiwa don tinkarar sauyin yanayi”, shawarar da ta bukaci kasashe masu ci gaba su taimaka wa kasashe masu fama da koma baya, wajen inganta kwarewarsu ta fannin tinkarar sauyin yanayi.

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

Ya zuwa ranar 22 ga watan Nuwamban, an kaddamar da taron kolin G20 a birnin Johannesburg na kasar Afirka ta Kudu, taron da ya kasance irinsa na farko da aka gudanar a nahiyar Afirka. Amma gwamnatin kasar Amurka ba ta halarci taron ba, har ma ta yi ta yi wa kasar Afirka ta Kudu mai masauki baki matsin lamba tun ba a fara taron ba, ta kuma ki yarda da taron ya bayar da sanarwa bisa taken daidaiton kungiyar G20 ba tare da samun amincewarta ba. Duk da hakan, mahalarta taron sun cimma daidaito a ranar farko da aka bude taron, har ma suka zartas da “sanarwar Johannesburg ta shugabannin G20” wadda ke kunshe da tanade-tanade 122, wanda hakan ya kafa sabon tarihin G20.

Lallai jerin abubuwa da suka wakana sun shaida yadda al’ummomin duniya ke rungumar hadin gwiwar cin moriyar juna a maimakon nuna fin karfi da ra’ayi na kashin kai. Zamanin da komai sai ya samu amincewar Amurka yana dab da karewa, kuma ana fitowa da sabon tsarin da kasa da kasa ke binsa a hadin gwiwarsu, yayin da suke kula da harkokin duniya. Yadda Amurka ke kauracewa tarukan bai haifar da komai ba, illa yin watsi da ita a fannin kulawa da harkokin duniya. Harkokin duniya na gudana yadda ya kamata, ko ba tare da Amurka ta sa hannu a ciki ba, kuma duniya za ta kara kyau in ba a nuna fin karfi.

 

 

 

Duniya
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
Duniya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Kama 'Yan Ta'adda 74, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace 318 A Watan Nuwamba 

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.