ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duniya Za Ta Kara Kyau In Ba A Nuna Fin Karfi

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
Duniya

Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya sanar a kwanan baya cewa, ba zai gayyaci Afirka ta Kudu ta halarci taron kolin kungiyar G20 da za a gudanar a birnin Miami na kasar Amurka a shekara mai zuwa ba.

Kasancewarsa muhimmin dandali na hadin gwiwar tattalin arzikin duniya, wakilci da hakuri su ne tushen kungiyar G20. Daga cikin kasashe mambobin kungiyar G20, kungiyar tarayyar Afirka (AU) da kuma kasar Afirka ta kudu, su biyu ne kadai suka fito daga nahiyar Afirka. Don haka, ba kawai kasar Afirka ta Kudu na wakiltar kanta ba ce, har ma tana dauke da nauyin fitar da muryar kasashen nahiyar game da gudanar harkokin tattalin arzikin duniya. Amma sai ga shi Amurka ta sanya bukatarta sama da matsayar sassan kasa da kasa, tana mai daukar odar duniya a matsayin wadda za ta iya takewa, tare da kallon hukumomin kasa da kasa a matsayin dan wasan dara da za ta iya sauyawa wuri a duk lokacin da take so, wanda hakan ya shaida yadda Amurka ke nuna fin karfi a duniya, da ma matsalar da ake fuskanta a tsarin kula da al’amuran duniya.

  • Ma’aikatan Shari’a Sun Fara Yajin Aiki Kan Bashin Albashi Da Kuɗin Hutu A Kogi
  • Ko Kwalliya Za Ta Biya Kuɗin Sabulu Kan Sauye-sauyen Tinubu Na Inganta Tsaro A Nijeriya?

Amma irin yanayi na nuna fin karfi da Amurka ke yi ba zai dore ba, ta la’akari da jerin wasu muhimman tarukan da aka gudanar a watan Nuwamban da ya gabata, wadanda suka samu muhimman nasarori ko da yake ba tare da hallarar kasar Amurka ba.

ADVERTISEMENT

A ranar 7 ga watan Nuwamban da ya gabata, hukumar kula da hakkin bil Adam ta MDD ta kira taron musamman, don yin nazari a kan harkokin hakkin bil Adam na kasar Amurka a karo na hudu. Tsarin nazarin harkokin hakkin dan Adam na kasa da kasa muhimmin tsari ne da MDD ta kafa don neman inganta musaya da hadin gwiwa a tsakanin kasa da kasa ta fannin kare hakkin dan Adam. Tun kafuwarsa a shekarar 2007, an gudanar da nazarin a kan kasashe mambobi 193 na MDD har sau uku, amma Amurka ta ki a yi mata sabon zagaye na nazarin. Duk da haka, sassan kasa da kasa sun tabbatar da gudanar tsarin nazarin ba tare da tsayawa ba, ta hanyar tsara sabon jadawali, da kuma gabatar da sabbin shawarwari, ta yadda tsarin kula da hakkin dan Adam na duniya zai kara kare adalci da samar da tasiri mai muhimmanci.

Haka nan kuma a ranar 10 ga watan Nuwamban, an gudanar da taron masu sa hannu a yarjejeniyar sauyin yanayi ta MDD (COP30) a birnin Belém na kasar Brazil. Amurka a matsayinta na kasar da ta fi yawan fitar da hayaki mai dumama yanayi a tarihi, ba ta tura wakilai masu babban matsayi zuwa taron ba, ban da wani mai taimakawa sakataren harkokin wajen kasar da ke kula da harkokin muhalli. Sai dai hakan bai haifar da cikas ga taron ba, bisa shawarwarin da mahalarta taron suka shafe tsawon kwanaki 13 suna yi, taron ya zartas da shawara mai taken “kira ga duniya: hadin gwiwa don tinkarar sauyin yanayi”, shawarar da ta bukaci kasashe masu ci gaba su taimaka wa kasashe masu fama da koma baya, wajen inganta kwarewarsu ta fannin tinkarar sauyin yanayi.

LABARAI MASU NASABA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

Ya zuwa ranar 22 ga watan Nuwamban, an kaddamar da taron kolin G20 a birnin Johannesburg na kasar Afirka ta Kudu, taron da ya kasance irinsa na farko da aka gudanar a nahiyar Afirka. Amma gwamnatin kasar Amurka ba ta halarci taron ba, har ma ta yi ta yi wa kasar Afirka ta Kudu mai masauki baki matsin lamba tun ba a fara taron ba, ta kuma ki yarda da taron ya bayar da sanarwa bisa taken daidaiton kungiyar G20 ba tare da samun amincewarta ba. Duk da hakan, mahalarta taron sun cimma daidaito a ranar farko da aka bude taron, har ma suka zartas da “sanarwar Johannesburg ta shugabannin G20” wadda ke kunshe da tanade-tanade 122, wanda hakan ya kafa sabon tarihin G20.

Lallai jerin abubuwa da suka wakana sun shaida yadda al’ummomin duniya ke rungumar hadin gwiwar cin moriyar juna a maimakon nuna fin karfi da ra’ayi na kashin kai. Zamanin da komai sai ya samu amincewar Amurka yana dab da karewa, kuma ana fitowa da sabon tsarin da kasa da kasa ke binsa a hadin gwiwarsu, yayin da suke kula da harkokin duniya. Yadda Amurka ke kauracewa tarukan bai haifar da komai ba, illa yin watsi da ita a fannin kulawa da harkokin duniya. Harkokin duniya na gudana yadda ya kamata, ko ba tare da Amurka ta sa hannu a ciki ba, kuma duniya za ta kara kyau in ba a nuna fin karfi.

 

 

 

Duniya
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
Duniya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Next Post
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Kama 'Yan Ta'adda 74, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace 318 A Watan Nuwamba 

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.