ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861 Na 2026 Ga Majalisar Dokokin Jihar Zamfara

by Sulaiman and Hussein Yero
7 months ago
Gwamna lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gabatar da ƙudirin kasafin kuɗi na shekarar 2026 mai darajar Naira Biliyan 861 ga Majalisar Dokokin Jihar, inda ya bayyana shi a matsayin taswirar sauyi da kuma shaida cewa Zamfara na kan hanyarta ta tashi tsaye da ƙarfi.

 

An gabatar da kasafin ne a ranar Alhamis a birnin Gusau.

ADVERTISEMENT
  • Duniya Za Ta Kara Kyau In Ba A Nuna Fin Karfi
  • Ma’aikatan Shari’a Sun Fara Yajin Aiki Kan Bashin Albashi Da Kuɗin Hutu A Kogi

A cikin sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, an bayyana cewa kasafin kuɗin ya ware Naira Biliyan 714, wato kashi 83 cikin 100, domin ayyukan raya ƙasa, yayin da aka ware Naira Biliyan 147.279 domin ayyukan yau da kullum na gwamnati, wanda ya kai kashi 17 cikin 100.

 

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Sanarwar ta ƙara da cewa, an tanadi Naira Biliyan 65 domin ilimi, Naira Biliyan 87 domin kiwon lafiyar al’umma, Naira Biliyan 86 a bangaren noma, Naira Biliyan 45 domin tabbatar da tsaro da zaman lafiya, Naira Biliyan 22 domin kare muhalli, sai Naira Biliyan 17 domin jin daɗin al’umma da tallafa musu.

 

A jawabinsa gaban majalisar, Gwamna Lawal ya ce gwamnatinsa, wadda aka zaba bisa alƙawarin ceto, gyara da farfaɗo da jihar, ta yi aiki tuƙuru wajen dawo da amincewa ga hukumomin gwamnati, gina manyan sassa, da shimfiɗa tubalin ci gaba mai ɗorewa.

 

Ya ce, mutanen Zamfara da a baya suka shiga damuwa sakamakon sakaci, yanzu sun fara ganin hasken gaskiya, ci gaba da sabon alƙibla.

 

Ya bayyana kasafin 2026 a matsayin sabon babi a wannan tafiya ta sauyi, yana mai cewa ba tsari ne na kuɗi kawai ba, illa allawari ne na siyasa da nufin tabbatar da zaman lafiya da kuma hanzarta bunƙasar da al’umma ke muradi.

 

A cewarsa, kasafin an tsara shi ne domin samun ribar tsare-tsaren shirin ceto na matakai shida da gwamnatinsa ke aiwatarwa, waɗanda suka haɗa da ƙarfafa tsaro, sabunta noma domin samar da wadatar abinci, inganta tsarin kiwon lafiya a kowane yanki, faɗaɗa damar samun nagartaccen ilimi, hanzarta raya ababen more rayuwa, da kuma ƙarfafa matasa, mata da masu rauni.

 

Gwamnan ya jaddada cewa kashi 17 na kuɗaɗen da aka ware domin kashe-kashen yau da kullum na nuna tsauraran matakan kula da kuɗi da kuma nagartar tafiyar da al’amuran gwamnati.

 

Ya ce, a ma’aunin ƙasa da kasa, ana ba da shawarar kada irin wannan kashe-kashe ya haura kashi 60, alhali Zamfara ta tsaya nesa da hakan, lamarin da ke nuna kyakyawan yanayin tafiyar da kuɗaɗe bisa ƙa’ida.

 

Ya kuma bayyana cewa, ginshiƙin kasafin shi ne ɓangaren ayyukan raya kasa da aka ware kashi 83, wanda ya kira tarihi, domin gina manyan ayyuka, karfafa tsaro, farfaɗo da noma, da kuma samar wa matasa damarmaki.

 

Gwamna Lawal ya ce, babu wani buri da za a cimma, daga tsaro zuwa ilimi, daga noma zuwa gine-gine, daga gyaran ma’aikata zuwa farfaɗo da tattalin arziki, face da cikakken goyon bayan siyasa, jajircewar gwamnati, da haɗa kai da majalisar dokoki.

 

A ƙarshe, ya miƙa kasafin kuɗi mai taken “Kasafin Tabbataccen Zaman Lafiya da Ci Gaba” na Naira biliyan 861.337 domin nazari da amincewa, yana mai cewa wannan kasafi yarjejeniya ce da al’umma, taswirar sauyi da kuma sanarwar cewa Zamfara za ta tashi tsaye da ƙarfi fiye da da.

Gwamna lawal
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Gwamna lawal
Hussein Yero
+ posts Bio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    ’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Ɗan Takarar Sanata A Zamfara Ya Koka Kan Yi Wa Rayuwarsa Barazana
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Abdulaziz Yari Ya Bukaci Limamai Su Ƙara Addu’a Kan Yaƙi Da Ƴan Bindiga A Zamfara

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Peng Liyuan Da Brigitte Macron Sun Ziyarci Gidan Wasannin Kwaikwayo Ta Al’umma Ta Beijing

Peng Liyuan Da Brigitte Macron Sun Ziyarci Gidan Wasannin Kwaikwayo Ta Al’umma Ta Beijing

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.