ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861 Na 2026 Ga Majalisar Dokokin Jihar Zamfara

by Sulaiman and Hussein Yero
6 months ago
Gwamna lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gabatar da ƙudirin kasafin kuɗi na shekarar 2026 mai darajar Naira Biliyan 861 ga Majalisar Dokokin Jihar, inda ya bayyana shi a matsayin taswirar sauyi da kuma shaida cewa Zamfara na kan hanyarta ta tashi tsaye da ƙarfi.

 

An gabatar da kasafin ne a ranar Alhamis a birnin Gusau.

ADVERTISEMENT
  • Duniya Za Ta Kara Kyau In Ba A Nuna Fin Karfi
  • Ma’aikatan Shari’a Sun Fara Yajin Aiki Kan Bashin Albashi Da Kuɗin Hutu A Kogi

A cikin sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, an bayyana cewa kasafin kuɗin ya ware Naira Biliyan 714, wato kashi 83 cikin 100, domin ayyukan raya ƙasa, yayin da aka ware Naira Biliyan 147.279 domin ayyukan yau da kullum na gwamnati, wanda ya kai kashi 17 cikin 100.

 

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Sanarwar ta ƙara da cewa, an tanadi Naira Biliyan 65 domin ilimi, Naira Biliyan 87 domin kiwon lafiyar al’umma, Naira Biliyan 86 a bangaren noma, Naira Biliyan 45 domin tabbatar da tsaro da zaman lafiya, Naira Biliyan 22 domin kare muhalli, sai Naira Biliyan 17 domin jin daɗin al’umma da tallafa musu.

 

A jawabinsa gaban majalisar, Gwamna Lawal ya ce gwamnatinsa, wadda aka zaba bisa alƙawarin ceto, gyara da farfaɗo da jihar, ta yi aiki tuƙuru wajen dawo da amincewa ga hukumomin gwamnati, gina manyan sassa, da shimfiɗa tubalin ci gaba mai ɗorewa.

 

Ya ce, mutanen Zamfara da a baya suka shiga damuwa sakamakon sakaci, yanzu sun fara ganin hasken gaskiya, ci gaba da sabon alƙibla.

 

Ya bayyana kasafin 2026 a matsayin sabon babi a wannan tafiya ta sauyi, yana mai cewa ba tsari ne na kuɗi kawai ba, illa allawari ne na siyasa da nufin tabbatar da zaman lafiya da kuma hanzarta bunƙasar da al’umma ke muradi.

 

A cewarsa, kasafin an tsara shi ne domin samun ribar tsare-tsaren shirin ceto na matakai shida da gwamnatinsa ke aiwatarwa, waɗanda suka haɗa da ƙarfafa tsaro, sabunta noma domin samar da wadatar abinci, inganta tsarin kiwon lafiya a kowane yanki, faɗaɗa damar samun nagartaccen ilimi, hanzarta raya ababen more rayuwa, da kuma ƙarfafa matasa, mata da masu rauni.

 

Gwamnan ya jaddada cewa kashi 17 na kuɗaɗen da aka ware domin kashe-kashen yau da kullum na nuna tsauraran matakan kula da kuɗi da kuma nagartar tafiyar da al’amuran gwamnati.

 

Ya ce, a ma’aunin ƙasa da kasa, ana ba da shawarar kada irin wannan kashe-kashe ya haura kashi 60, alhali Zamfara ta tsaya nesa da hakan, lamarin da ke nuna kyakyawan yanayin tafiyar da kuɗaɗe bisa ƙa’ida.

 

Ya kuma bayyana cewa, ginshiƙin kasafin shi ne ɓangaren ayyukan raya kasa da aka ware kashi 83, wanda ya kira tarihi, domin gina manyan ayyuka, karfafa tsaro, farfaɗo da noma, da kuma samar wa matasa damarmaki.

 

Gwamna Lawal ya ce, babu wani buri da za a cimma, daga tsaro zuwa ilimi, daga noma zuwa gine-gine, daga gyaran ma’aikata zuwa farfaɗo da tattalin arziki, face da cikakken goyon bayan siyasa, jajircewar gwamnati, da haɗa kai da majalisar dokoki.

 

A ƙarshe, ya miƙa kasafin kuɗi mai taken “Kasafin Tabbataccen Zaman Lafiya da Ci Gaba” na Naira biliyan 861.337 domin nazari da amincewa, yana mai cewa wannan kasafi yarjejeniya ce da al’umma, taswirar sauyi da kuma sanarwar cewa Zamfara za ta tashi tsaye da ƙarfi fiye da da.

Gwamna lawal
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP
Gwamna lawal
Hussein Yero
+ posts Bio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Ɗan Takarar Sanata A Zamfara Ya Koka Kan Yi Wa Rayuwarsa Barazana
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Abdulaziz Yari Ya Bukaci Limamai Su Ƙara Addu’a Kan Yaƙi Da Ƴan Bindiga A Zamfara
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Matawalle Ya Buƙaci Magoya Bayansa Su Mara Wa Shugaba Tinubu, Gwamna Lawal Baya
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Majalisar Zamfara Ta Dakatar Da Shugabannin Kananan Hukumomi Biyu Kan Zargin Almundahanar Kuɗaɗe

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Peng Liyuan Da Brigitte Macron Sun Ziyarci Gidan Wasannin Kwaikwayo Ta Al’umma Ta Beijing

Peng Liyuan Da Brigitte Macron Sun Ziyarci Gidan Wasannin Kwaikwayo Ta Al’umma Ta Beijing

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.