ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861 Na 2026 Ga Majalisar Dokokin Jihar Zamfara

by Sulaiman and Hussein Yero
7 months ago
Gwamna lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gabatar da ƙudirin kasafin kuɗi na shekarar 2026 mai darajar Naira Biliyan 861 ga Majalisar Dokokin Jihar, inda ya bayyana shi a matsayin taswirar sauyi da kuma shaida cewa Zamfara na kan hanyarta ta tashi tsaye da ƙarfi.

 

An gabatar da kasafin ne a ranar Alhamis a birnin Gusau.

ADVERTISEMENT
  • Duniya Za Ta Kara Kyau In Ba A Nuna Fin Karfi
  • Ma’aikatan Shari’a Sun Fara Yajin Aiki Kan Bashin Albashi Da Kuɗin Hutu A Kogi

A cikin sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, an bayyana cewa kasafin kuɗin ya ware Naira Biliyan 714, wato kashi 83 cikin 100, domin ayyukan raya ƙasa, yayin da aka ware Naira Biliyan 147.279 domin ayyukan yau da kullum na gwamnati, wanda ya kai kashi 17 cikin 100.

 

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sanarwar ta ƙara da cewa, an tanadi Naira Biliyan 65 domin ilimi, Naira Biliyan 87 domin kiwon lafiyar al’umma, Naira Biliyan 86 a bangaren noma, Naira Biliyan 45 domin tabbatar da tsaro da zaman lafiya, Naira Biliyan 22 domin kare muhalli, sai Naira Biliyan 17 domin jin daɗin al’umma da tallafa musu.

 

A jawabinsa gaban majalisar, Gwamna Lawal ya ce gwamnatinsa, wadda aka zaba bisa alƙawarin ceto, gyara da farfaɗo da jihar, ta yi aiki tuƙuru wajen dawo da amincewa ga hukumomin gwamnati, gina manyan sassa, da shimfiɗa tubalin ci gaba mai ɗorewa.

 

Ya ce, mutanen Zamfara da a baya suka shiga damuwa sakamakon sakaci, yanzu sun fara ganin hasken gaskiya, ci gaba da sabon alƙibla.

 

Ya bayyana kasafin 2026 a matsayin sabon babi a wannan tafiya ta sauyi, yana mai cewa ba tsari ne na kuɗi kawai ba, illa allawari ne na siyasa da nufin tabbatar da zaman lafiya da kuma hanzarta bunƙasar da al’umma ke muradi.

 

A cewarsa, kasafin an tsara shi ne domin samun ribar tsare-tsaren shirin ceto na matakai shida da gwamnatinsa ke aiwatarwa, waɗanda suka haɗa da ƙarfafa tsaro, sabunta noma domin samar da wadatar abinci, inganta tsarin kiwon lafiya a kowane yanki, faɗaɗa damar samun nagartaccen ilimi, hanzarta raya ababen more rayuwa, da kuma ƙarfafa matasa, mata da masu rauni.

 

Gwamnan ya jaddada cewa kashi 17 na kuɗaɗen da aka ware domin kashe-kashen yau da kullum na nuna tsauraran matakan kula da kuɗi da kuma nagartar tafiyar da al’amuran gwamnati.

 

Ya ce, a ma’aunin ƙasa da kasa, ana ba da shawarar kada irin wannan kashe-kashe ya haura kashi 60, alhali Zamfara ta tsaya nesa da hakan, lamarin da ke nuna kyakyawan yanayin tafiyar da kuɗaɗe bisa ƙa’ida.

 

Ya kuma bayyana cewa, ginshiƙin kasafin shi ne ɓangaren ayyukan raya kasa da aka ware kashi 83, wanda ya kira tarihi, domin gina manyan ayyuka, karfafa tsaro, farfaɗo da noma, da kuma samar wa matasa damarmaki.

 

Gwamna Lawal ya ce, babu wani buri da za a cimma, daga tsaro zuwa ilimi, daga noma zuwa gine-gine, daga gyaran ma’aikata zuwa farfaɗo da tattalin arziki, face da cikakken goyon bayan siyasa, jajircewar gwamnati, da haɗa kai da majalisar dokoki.

 

A ƙarshe, ya miƙa kasafin kuɗi mai taken “Kasafin Tabbataccen Zaman Lafiya da Ci Gaba” na Naira biliyan 861.337 domin nazari da amincewa, yana mai cewa wannan kasafi yarjejeniya ce da al’umma, taswirar sauyi da kuma sanarwar cewa Zamfara za ta tashi tsaye da ƙarfi fiye da da.

Gwamna lawal
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya
Gwamna lawal
Hussein Yero
+ posts Bio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    ’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Ɗan Takarar Sanata A Zamfara Ya Koka Kan Yi Wa Rayuwarsa Barazana
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Abdulaziz Yari Ya Bukaci Limamai Su Ƙara Addu’a Kan Yaƙi Da Ƴan Bindiga A Zamfara

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Next Post
Peng Liyuan Da Brigitte Macron Sun Ziyarci Gidan Wasannin Kwaikwayo Ta Al’umma Ta Beijing

Peng Liyuan Da Brigitte Macron Sun Ziyarci Gidan Wasannin Kwaikwayo Ta Al’umma Ta Beijing

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.