ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarayyar Turai Ta Ɗauki Nauyin Shirin Zaman Lafiya Na Yuro Miliyan 5.1 A Zamfara

by Sulaiman
5 days ago
Turai

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ƙaddamar da wani sabon gagarumin shirin Tarayyar Turai da darajar sa ta kai ma tsabar kuɗi Yuro Miliyan 5.1, wanda aka tsara domin ƙarfafa zaman lafiya, kwanciyar hankali da juriyar al’umma a yankunan da rikice-rikice suka fi shafa a Zamfara da Katsina.

 

An ƙaddamar da shirin mai suna ‘Conflict Prevention, Crisis Response and Resilience’ (CPCRR) ne a ranar Litinin a ɗakin taro na Rescue Hall da ke Gidan Gwamnati a Gusau, inda Tarayyar Turai ta bayyana cikakken goyon bayanta ga ƙoƙarin gwamnatin Zamfara na dawo da zaman lafiya mai ɗorewa.

ADVERTISEMENT
  • Shugaba Xi Ya Saurari Rahoton Aiki Daga Kantoman Yankin Musamman Na Hong Kong
  • Da Ɗumi ɗumi: Mafarkin Nijeriya Na Zuwa Gasar Kofin Duniya Na Dab Da Cika

Wata sanarwa da kakakin gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta ce Gautier Mignot, Jakadan Tarayyar Turai a Nijeriya, ya halarci taron ƙaddamar da shirin wanda zai gudana tsawon watanni 18.

 

LABARAI MASU NASABA

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

Sanarwar ta ƙara da cewa, tawagar jakadan ta haɗa da shugabar Hukumar Ƙaura ta Duniya, wato ‘International Organization for Migration’, Dimanche Sharon, da shugaban IOM na yankin Arewa maso Yamma, Jean Nahesi Katumbakana.

 

Shirin na CPCRR, wanda EU ke ɗaukar nauyin sa tare da aiwatarwa ta hannun IOM tare da haɗin gwiwar Mercy Corps da Cibiyar Raya Dimokuraɗiyya (CDD), an tsara shi ne domin tallafa wa sama da mutane 95,000 kai tsaye.

 

Waɗanda za su amfana sun haɗa da ‘yan gudun hijira na cikin gida, masu komawa muhallansu, al’ummomin da ke karɓar baƙi, mata da matasa a ƙananan hukumomi goma, takwas a Katsina da biyu a Zamfara.

 

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Lawal ya bayyana cewa muhimmancin shirin bai tsaya a kan takardu ko jadawalin ayyuka kawai ba, sai dai yana shafar rayuwar yau da kullum ta jama’a.

 

Ya ce, shirin yana nuna aniyar haɗin kai tsakanin gwamnatin jihar da abokan hulɗa na ƙasa da ƙasa wajen gina al’umma mai ƙarfi, haɗin kai da zaman lafiya.

 

Gwamnan ya jaddada cewa tun farkon wannan gwamnati, an ɗauki batun tsaro da muhimmanci ta fuskar fahimtar tushen matsalolin da ke haifar da rikice-rikice, ciki har da talauci, raunin cibiyoyi da rushewar amincewar jama’a da juna.

 

A cewarsa, waɗannan su ne ginshiƙan da ake la’akari da su wajen tsara manufofi da haɗin gwiwa da abokan ci gaba.

 

Ya ƙara da cewa, shirin na CPCRR zai cike gibin ƙoƙarin gwamnatin Zamfara wajen farfaɗo da tattalin arzikin matasa da mata, inganta haɗin kai tsakanin ma’aikatu da hukumomi, da kuma tallafa wa hanyoyin tattaunawar sulhu a matakin al’umma, bisa fahimtar cewa tsaro, ci gaba da kyakkyawan shugabanci suna tafiya tare.

 

A nasa jawabin, Jakadan Tarayyar Turai, Gautier Mignot, ya yaba wa Gwamna Lawal kan jajircewarsa da goyon bayan da yake bai wa abokan ci gaba, yana mai bayyana kwarin gwiwar EU cewa wannan shiri zai taimaka wajen samar da Zamfara mai kwanciyar hankali da makoma mai kyau.

 

A ƙarshe, Gwamna Lawal ya gode wa Tarayyar Turai da IOM tare da CDD da Mercy Corps, yana mai cewa gina zaman lafiya aiki ne na bai ɗaya da ke buƙatar haɗin kan kowane ɓangare na al’umma. Daga nan ya sanar da fara aiwatar da shirin CPCRR a hukumance a Zamfara.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa
Labarai

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli
Labarai

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Next Post
Shugaba Xi Ya Saurari Rahoton Aiki Daga Kantoman Yankin Musamman Na Macao

Shugaba Xi Ya Saurari Rahoton Aiki Daga Kantoman Yankin Musamman Na Macao

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.