ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarayyar Turai Ta Ɗauki Nauyin Shirin Zaman Lafiya Na Yuro Miliyan 5.1 A Zamfara

by Sulaiman
6 months ago
Turai

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ƙaddamar da wani sabon gagarumin shirin Tarayyar Turai da darajar sa ta kai ma tsabar kuɗi Yuro Miliyan 5.1, wanda aka tsara domin ƙarfafa zaman lafiya, kwanciyar hankali da juriyar al’umma a yankunan da rikice-rikice suka fi shafa a Zamfara da Katsina.

 

An ƙaddamar da shirin mai suna ‘Conflict Prevention, Crisis Response and Resilience’ (CPCRR) ne a ranar Litinin a ɗakin taro na Rescue Hall da ke Gidan Gwamnati a Gusau, inda Tarayyar Turai ta bayyana cikakken goyon bayanta ga ƙoƙarin gwamnatin Zamfara na dawo da zaman lafiya mai ɗorewa.

ADVERTISEMENT
  • Shugaba Xi Ya Saurari Rahoton Aiki Daga Kantoman Yankin Musamman Na Hong Kong
  • Da Ɗumi ɗumi: Mafarkin Nijeriya Na Zuwa Gasar Kofin Duniya Na Dab Da Cika

Wata sanarwa da kakakin gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta ce Gautier Mignot, Jakadan Tarayyar Turai a Nijeriya, ya halarci taron ƙaddamar da shirin wanda zai gudana tsawon watanni 18.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sanarwar ta ƙara da cewa, tawagar jakadan ta haɗa da shugabar Hukumar Ƙaura ta Duniya, wato ‘International Organization for Migration’, Dimanche Sharon, da shugaban IOM na yankin Arewa maso Yamma, Jean Nahesi Katumbakana.

 

Shirin na CPCRR, wanda EU ke ɗaukar nauyin sa tare da aiwatarwa ta hannun IOM tare da haɗin gwiwar Mercy Corps da Cibiyar Raya Dimokuraɗiyya (CDD), an tsara shi ne domin tallafa wa sama da mutane 95,000 kai tsaye.

 

Waɗanda za su amfana sun haɗa da ‘yan gudun hijira na cikin gida, masu komawa muhallansu, al’ummomin da ke karɓar baƙi, mata da matasa a ƙananan hukumomi goma, takwas a Katsina da biyu a Zamfara.

 

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Lawal ya bayyana cewa muhimmancin shirin bai tsaya a kan takardu ko jadawalin ayyuka kawai ba, sai dai yana shafar rayuwar yau da kullum ta jama’a.

 

Ya ce, shirin yana nuna aniyar haɗin kai tsakanin gwamnatin jihar da abokan hulɗa na ƙasa da ƙasa wajen gina al’umma mai ƙarfi, haɗin kai da zaman lafiya.

 

Gwamnan ya jaddada cewa tun farkon wannan gwamnati, an ɗauki batun tsaro da muhimmanci ta fuskar fahimtar tushen matsalolin da ke haifar da rikice-rikice, ciki har da talauci, raunin cibiyoyi da rushewar amincewar jama’a da juna.

 

A cewarsa, waɗannan su ne ginshiƙan da ake la’akari da su wajen tsara manufofi da haɗin gwiwa da abokan ci gaba.

 

Ya ƙara da cewa, shirin na CPCRR zai cike gibin ƙoƙarin gwamnatin Zamfara wajen farfaɗo da tattalin arzikin matasa da mata, inganta haɗin kai tsakanin ma’aikatu da hukumomi, da kuma tallafa wa hanyoyin tattaunawar sulhu a matakin al’umma, bisa fahimtar cewa tsaro, ci gaba da kyakkyawan shugabanci suna tafiya tare.

 

A nasa jawabin, Jakadan Tarayyar Turai, Gautier Mignot, ya yaba wa Gwamna Lawal kan jajircewarsa da goyon bayan da yake bai wa abokan ci gaba, yana mai bayyana kwarin gwiwar EU cewa wannan shiri zai taimaka wajen samar da Zamfara mai kwanciyar hankali da makoma mai kyau.

 

A ƙarshe, Gwamna Lawal ya gode wa Tarayyar Turai da IOM tare da CDD da Mercy Corps, yana mai cewa gina zaman lafiya aiki ne na bai ɗaya da ke buƙatar haɗin kan kowane ɓangare na al’umma. Daga nan ya sanar da fara aiwatar da shirin CPCRR a hukumance a Zamfara.

Turai
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Shugaba Xi Ya Saurari Rahoton Aiki Daga Kantoman Yankin Musamman Na Macao

Shugaba Xi Ya Saurari Rahoton Aiki Daga Kantoman Yankin Musamman Na Macao

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.