ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarayyar Turai Ta Ɗauki Nauyin Shirin Zaman Lafiya Na Yuro Miliyan 5.1 A Zamfara

by Sulaiman
9 months ago
Turai

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ƙaddamar da wani sabon gagarumin shirin Tarayyar Turai da darajar sa ta kai ma tsabar kuɗi Yuro Miliyan 5.1, wanda aka tsara domin ƙarfafa zaman lafiya, kwanciyar hankali da juriyar al’umma a yankunan da rikice-rikice suka fi shafa a Zamfara da Katsina.

 

An ƙaddamar da shirin mai suna ‘Conflict Prevention, Crisis Response and Resilience’ (CPCRR) ne a ranar Litinin a ɗakin taro na Rescue Hall da ke Gidan Gwamnati a Gusau, inda Tarayyar Turai ta bayyana cikakken goyon bayanta ga ƙoƙarin gwamnatin Zamfara na dawo da zaman lafiya mai ɗorewa.

ADVERTISEMENT
  • Shugaba Xi Ya Saurari Rahoton Aiki Daga Kantoman Yankin Musamman Na Hong Kong
  • Da Ɗumi ɗumi: Mafarkin Nijeriya Na Zuwa Gasar Kofin Duniya Na Dab Da Cika

Wata sanarwa da kakakin gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta ce Gautier Mignot, Jakadan Tarayyar Turai a Nijeriya, ya halarci taron ƙaddamar da shirin wanda zai gudana tsawon watanni 18.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Sanarwar ta ƙara da cewa, tawagar jakadan ta haɗa da shugabar Hukumar Ƙaura ta Duniya, wato ‘International Organization for Migration’, Dimanche Sharon, da shugaban IOM na yankin Arewa maso Yamma, Jean Nahesi Katumbakana.

 

Shirin na CPCRR, wanda EU ke ɗaukar nauyin sa tare da aiwatarwa ta hannun IOM tare da haɗin gwiwar Mercy Corps da Cibiyar Raya Dimokuraɗiyya (CDD), an tsara shi ne domin tallafa wa sama da mutane 95,000 kai tsaye.

 

Waɗanda za su amfana sun haɗa da ‘yan gudun hijira na cikin gida, masu komawa muhallansu, al’ummomin da ke karɓar baƙi, mata da matasa a ƙananan hukumomi goma, takwas a Katsina da biyu a Zamfara.

 

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Lawal ya bayyana cewa muhimmancin shirin bai tsaya a kan takardu ko jadawalin ayyuka kawai ba, sai dai yana shafar rayuwar yau da kullum ta jama’a.

 

Ya ce, shirin yana nuna aniyar haɗin kai tsakanin gwamnatin jihar da abokan hulɗa na ƙasa da ƙasa wajen gina al’umma mai ƙarfi, haɗin kai da zaman lafiya.

 

Gwamnan ya jaddada cewa tun farkon wannan gwamnati, an ɗauki batun tsaro da muhimmanci ta fuskar fahimtar tushen matsalolin da ke haifar da rikice-rikice, ciki har da talauci, raunin cibiyoyi da rushewar amincewar jama’a da juna.

 

A cewarsa, waɗannan su ne ginshiƙan da ake la’akari da su wajen tsara manufofi da haɗin gwiwa da abokan ci gaba.

 

Ya ƙara da cewa, shirin na CPCRR zai cike gibin ƙoƙarin gwamnatin Zamfara wajen farfaɗo da tattalin arzikin matasa da mata, inganta haɗin kai tsakanin ma’aikatu da hukumomi, da kuma tallafa wa hanyoyin tattaunawar sulhu a matakin al’umma, bisa fahimtar cewa tsaro, ci gaba da kyakkyawan shugabanci suna tafiya tare.

 

A nasa jawabin, Jakadan Tarayyar Turai, Gautier Mignot, ya yaba wa Gwamna Lawal kan jajircewarsa da goyon bayan da yake bai wa abokan ci gaba, yana mai bayyana kwarin gwiwar EU cewa wannan shiri zai taimaka wajen samar da Zamfara mai kwanciyar hankali da makoma mai kyau.

 

A ƙarshe, Gwamna Lawal ya gode wa Tarayyar Turai da IOM tare da CDD da Mercy Corps, yana mai cewa gina zaman lafiya aiki ne na bai ɗaya da ke buƙatar haɗin kan kowane ɓangare na al’umma. Daga nan ya sanar da fara aiwatar da shirin CPCRR a hukumance a Zamfara.

Turai
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Shugaba Xi Ya Saurari Rahoton Aiki Daga Kantoman Yankin Musamman Na Macao

Shugaba Xi Ya Saurari Rahoton Aiki Daga Kantoman Yankin Musamman Na Macao

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.