ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Marigayi Shugaba Buhari Ya Yi Zargin Na Yi Shirin Kashe Shi —Aisha Buhari

by Rabi'u Ali Indabawa
2 days ago
Aisha

Tsohuwar Uwargidan Shugaban Kasa, Aisha Buhari, ta bayyana cewa jita-jita da suka yadu a cikin Fadar Shugaban Kasa (Billa) a wani lokaci sun sa marigayi mijinta, Muhammadu Buhari, ya fara zargin cewa tana shirin cutar da shi.

Ta ce wannan lamari ya dagula tsarin cin abincinsa tare da ba da gudummawa ga matsalar rashin lafiyar da ta sa ya kaurace wa gudanar da aiki na tsawon watanni a shekarar 2017.

  • Wang Yi Ya Zanta Da Ministocin Wajen Cambodia Da Thailand 
  • Tinubu Zai Gabatar Da Daftarin Kasafin Kuɗin 2026 Ga Majalisun Tarayya

Bayaninta na kunshe ne a cikin sabon littafin tarihin rayuwa mai taken ‘From Soldier to Statesman: The Legacy of Muhammadu Buhari.’ Charles Omole ne ya rubuta littafin, kuma an kaddamar da shi a Fadar Gwamnati (State House) ranar Litinin.

ADVERTISEMENT

A cewar littafin, Misis Buhari ta ce jita-jitar ta tayar da fargaba a cikin Aso Rock ta haifar da dan rashin amincewa a tsakaninta da Shugaban Kasar na dan wani lokaci.

Ta ce lamarin ya sa ya sauya wasu dabi’unsa na kashin kai, ciki har da kulle dakinsa da kuma rasa wasu lokutan cin abinci. Tsohuwar uwargidan shugaban kasa ta ce tangardar da aka samu a tsarin abinci da aka tsara da kulawa sosai ita ce farkon rashin lafiyarsa.

LABARAI MASU NASABA

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

Mrs Buhari ta bayyana cewa tsawon shekaru ita da kanta take sa ido kan abincin Buhari da karin magunguna (supplements) da yake sha, tsarin da ta ce ya zama dole domin kula da lafiyarsa.

“Wannan ya kasance ne duba da dogon tarihinsa na matsalolin abinci. Rashin lafiyar Buhari ba ta kasance abin asiri ba kuma ba sakamakon guba ba ce,” in ji ta.

Littafin ya bayyana cewa bayan sun kaura daga Kaduna zuwa Fadar Shugaban Kasa, alhakin kula da tsarin abincin Buhari ya koma hannun jami’an gwamnati, lamarin da ya haifar da jinkiri, tsallake lokutan cin abinci, da kuma dakatar da karin magungunan da aka rubuta masa.

A cewar Aisha a cikin littafin, tsawon kusan shekara guda Shugaban Kasar ya daina cin abincin rana akai-akai, inda ta kara da cewa rugujewar tsarin kula da abinci ya raunana shi matuka. Ta ce wannan tabarbarewar ce daga bisani ta haifar da dogwayen tafiye-tafiyen jinya na Buhari zuwa Kasar Birtaniya a shekarar 2017, wadanda suka kai jimillar kwanaki 154, a lokacin da ya mika ikon shugabanci ga Mataimakin Shugaban Kasa, Yemi Osinbajo.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa
Labarai

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli
Labarai

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Next Post
Hidimar Kwastam Mai Zaman Kanta Da Sin Ta Kafa Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Masu Zuba Jari Na Waje

Hidimar Kwastam Mai Zaman Kanta Da Sin Ta Kafa Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Masu Zuba Jari Na Waje

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.