ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Marigayi Shugaba Buhari Ya Yi Zargin Na Yi Shirin Kashe Shi —Aisha Buhari

by Rabi'u Ali Indabawa
9 months ago
Aisha

Tsohuwar Uwargidan Shugaban Kasa, Aisha Buhari, ta bayyana cewa jita-jita da suka yadu a cikin Fadar Shugaban Kasa (Billa) a wani lokaci sun sa marigayi mijinta, Muhammadu Buhari, ya fara zargin cewa tana shirin cutar da shi.

Ta ce wannan lamari ya dagula tsarin cin abincinsa tare da ba da gudummawa ga matsalar rashin lafiyar da ta sa ya kaurace wa gudanar da aiki na tsawon watanni a shekarar 2017.

  • Wang Yi Ya Zanta Da Ministocin Wajen Cambodia Da Thailand 
  • Tinubu Zai Gabatar Da Daftarin Kasafin Kuɗin 2026 Ga Majalisun Tarayya

Bayaninta na kunshe ne a cikin sabon littafin tarihin rayuwa mai taken ‘From Soldier to Statesman: The Legacy of Muhammadu Buhari.’ Charles Omole ne ya rubuta littafin, kuma an kaddamar da shi a Fadar Gwamnati (State House) ranar Litinin.

ADVERTISEMENT

A cewar littafin, Misis Buhari ta ce jita-jitar ta tayar da fargaba a cikin Aso Rock ta haifar da dan rashin amincewa a tsakaninta da Shugaban Kasar na dan wani lokaci.

Ta ce lamarin ya sa ya sauya wasu dabi’unsa na kashin kai, ciki har da kulle dakinsa da kuma rasa wasu lokutan cin abinci. Tsohuwar uwargidan shugaban kasa ta ce tangardar da aka samu a tsarin abinci da aka tsara da kulawa sosai ita ce farkon rashin lafiyarsa.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Mrs Buhari ta bayyana cewa tsawon shekaru ita da kanta take sa ido kan abincin Buhari da karin magunguna (supplements) da yake sha, tsarin da ta ce ya zama dole domin kula da lafiyarsa.

“Wannan ya kasance ne duba da dogon tarihinsa na matsalolin abinci. Rashin lafiyar Buhari ba ta kasance abin asiri ba kuma ba sakamakon guba ba ce,” in ji ta.

Littafin ya bayyana cewa bayan sun kaura daga Kaduna zuwa Fadar Shugaban Kasa, alhakin kula da tsarin abincin Buhari ya koma hannun jami’an gwamnati, lamarin da ya haifar da jinkiri, tsallake lokutan cin abinci, da kuma dakatar da karin magungunan da aka rubuta masa.

A cewar Aisha a cikin littafin, tsawon kusan shekara guda Shugaban Kasar ya daina cin abincin rana akai-akai, inda ta kara da cewa rugujewar tsarin kula da abinci ya raunana shi matuka. Ta ce wannan tabarbarewar ce daga bisani ta haifar da dogwayen tafiye-tafiyen jinya na Buhari zuwa Kasar Birtaniya a shekarar 2017, wadanda suka kai jimillar kwanaki 154, a lokacin da ya mika ikon shugabanci ga Mataimakin Shugaban Kasa, Yemi Osinbajo.

Aisha
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Hidimar Kwastam Mai Zaman Kanta Da Sin Ta Kafa Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Masu Zuba Jari Na Waje

Hidimar Kwastam Mai Zaman Kanta Da Sin Ta Kafa Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Masu Zuba Jari Na Waje

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.