ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Marigayi Shugaba Buhari Ya Yi Zargin Na Yi Shirin Kashe Shi —Aisha Buhari

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
Aisha

Tsohuwar Uwargidan Shugaban Kasa, Aisha Buhari, ta bayyana cewa jita-jita da suka yadu a cikin Fadar Shugaban Kasa (Billa) a wani lokaci sun sa marigayi mijinta, Muhammadu Buhari, ya fara zargin cewa tana shirin cutar da shi.

Ta ce wannan lamari ya dagula tsarin cin abincinsa tare da ba da gudummawa ga matsalar rashin lafiyar da ta sa ya kaurace wa gudanar da aiki na tsawon watanni a shekarar 2017.

  • Wang Yi Ya Zanta Da Ministocin Wajen Cambodia Da Thailand 
  • Tinubu Zai Gabatar Da Daftarin Kasafin Kuɗin 2026 Ga Majalisun Tarayya

Bayaninta na kunshe ne a cikin sabon littafin tarihin rayuwa mai taken ‘From Soldier to Statesman: The Legacy of Muhammadu Buhari.’ Charles Omole ne ya rubuta littafin, kuma an kaddamar da shi a Fadar Gwamnati (State House) ranar Litinin.

ADVERTISEMENT

A cewar littafin, Misis Buhari ta ce jita-jitar ta tayar da fargaba a cikin Aso Rock ta haifar da dan rashin amincewa a tsakaninta da Shugaban Kasar na dan wani lokaci.

Ta ce lamarin ya sa ya sauya wasu dabi’unsa na kashin kai, ciki har da kulle dakinsa da kuma rasa wasu lokutan cin abinci. Tsohuwar uwargidan shugaban kasa ta ce tangardar da aka samu a tsarin abinci da aka tsara da kulawa sosai ita ce farkon rashin lafiyarsa.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Mrs Buhari ta bayyana cewa tsawon shekaru ita da kanta take sa ido kan abincin Buhari da karin magunguna (supplements) da yake sha, tsarin da ta ce ya zama dole domin kula da lafiyarsa.

“Wannan ya kasance ne duba da dogon tarihinsa na matsalolin abinci. Rashin lafiyar Buhari ba ta kasance abin asiri ba kuma ba sakamakon guba ba ce,” in ji ta.

Littafin ya bayyana cewa bayan sun kaura daga Kaduna zuwa Fadar Shugaban Kasa, alhakin kula da tsarin abincin Buhari ya koma hannun jami’an gwamnati, lamarin da ya haifar da jinkiri, tsallake lokutan cin abinci, da kuma dakatar da karin magungunan da aka rubuta masa.

A cewar Aisha a cikin littafin, tsawon kusan shekara guda Shugaban Kasar ya daina cin abincin rana akai-akai, inda ta kara da cewa rugujewar tsarin kula da abinci ya raunana shi matuka. Ta ce wannan tabarbarewar ce daga bisani ta haifar da dogwayen tafiye-tafiyen jinya na Buhari zuwa Kasar Birtaniya a shekarar 2017, wadanda suka kai jimillar kwanaki 154, a lokacin da ya mika ikon shugabanci ga Mataimakin Shugaban Kasa, Yemi Osinbajo.

Aisha
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Hidimar Kwastam Mai Zaman Kanta Da Sin Ta Kafa Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Masu Zuba Jari Na Waje

Hidimar Kwastam Mai Zaman Kanta Da Sin Ta Kafa Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Masu Zuba Jari Na Waje

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.