ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Marigayi Shugaba Buhari Ya Yi Zargin Na Yi Shirin Kashe Shi —Aisha Buhari

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
Aisha

Tsohuwar Uwargidan Shugaban Kasa, Aisha Buhari, ta bayyana cewa jita-jita da suka yadu a cikin Fadar Shugaban Kasa (Billa) a wani lokaci sun sa marigayi mijinta, Muhammadu Buhari, ya fara zargin cewa tana shirin cutar da shi.

Ta ce wannan lamari ya dagula tsarin cin abincinsa tare da ba da gudummawa ga matsalar rashin lafiyar da ta sa ya kaurace wa gudanar da aiki na tsawon watanni a shekarar 2017.

  • Wang Yi Ya Zanta Da Ministocin Wajen Cambodia Da Thailand 
  • Tinubu Zai Gabatar Da Daftarin Kasafin Kuɗin 2026 Ga Majalisun Tarayya

Bayaninta na kunshe ne a cikin sabon littafin tarihin rayuwa mai taken ‘From Soldier to Statesman: The Legacy of Muhammadu Buhari.’ Charles Omole ne ya rubuta littafin, kuma an kaddamar da shi a Fadar Gwamnati (State House) ranar Litinin.

ADVERTISEMENT

A cewar littafin, Misis Buhari ta ce jita-jitar ta tayar da fargaba a cikin Aso Rock ta haifar da dan rashin amincewa a tsakaninta da Shugaban Kasar na dan wani lokaci.

Ta ce lamarin ya sa ya sauya wasu dabi’unsa na kashin kai, ciki har da kulle dakinsa da kuma rasa wasu lokutan cin abinci. Tsohuwar uwargidan shugaban kasa ta ce tangardar da aka samu a tsarin abinci da aka tsara da kulawa sosai ita ce farkon rashin lafiyarsa.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Mrs Buhari ta bayyana cewa tsawon shekaru ita da kanta take sa ido kan abincin Buhari da karin magunguna (supplements) da yake sha, tsarin da ta ce ya zama dole domin kula da lafiyarsa.

“Wannan ya kasance ne duba da dogon tarihinsa na matsalolin abinci. Rashin lafiyar Buhari ba ta kasance abin asiri ba kuma ba sakamakon guba ba ce,” in ji ta.

Littafin ya bayyana cewa bayan sun kaura daga Kaduna zuwa Fadar Shugaban Kasa, alhakin kula da tsarin abincin Buhari ya koma hannun jami’an gwamnati, lamarin da ya haifar da jinkiri, tsallake lokutan cin abinci, da kuma dakatar da karin magungunan da aka rubuta masa.

A cewar Aisha a cikin littafin, tsawon kusan shekara guda Shugaban Kasar ya daina cin abincin rana akai-akai, inda ta kara da cewa rugujewar tsarin kula da abinci ya raunana shi matuka. Ta ce wannan tabarbarewar ce daga bisani ta haifar da dogwayen tafiye-tafiyen jinya na Buhari zuwa Kasar Birtaniya a shekarar 2017, wadanda suka kai jimillar kwanaki 154, a lokacin da ya mika ikon shugabanci ga Mataimakin Shugaban Kasa, Yemi Osinbajo.

Aisha
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Hidimar Kwastam Mai Zaman Kanta Da Sin Ta Kafa Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Masu Zuba Jari Na Waje

Hidimar Kwastam Mai Zaman Kanta Da Sin Ta Kafa Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Masu Zuba Jari Na Waje

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.