• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Kyakkyawa Za Ta Kara Samar Da Gudummawarta Ga Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

Karancin makamashi matsala ce da galibin kasashen Afirka ke fuskanta, a yayin da kuma nahiyar Afirka ta kasance daya daga cikin sassan duniya da suke karancin karfin tinkarar sauyin yanayi, don haka, ya zama dole kasashen Afirka su bunkasa makamashi mai tsabta a wani kokari na tabbatar da dauwamammen ci gabansu.

A watan Afrilun bana, rukunin na’urori na farko ya fara samar da wutar lantarki a madatsar ruwa ta Zungeru da ke kogin Kaduna na jihar Niger ta kasar Nijeriya, tasha ce da kamfanin kasar Sin ya gina, wadda ake sa ran zata iya samar da wutar lantarki da zai biya bukatun birane biyu da girmansu ya kai kamar na babban birnin Abuja, wadda kuma za ta taimaka ga kyautata matsalar karancin wuta da ake fuskanta a kasar, da ma tabbatar da dauwamammen ci gaban kasar.
A hakika, tuni kasar Sin ta aiwatar da shirye-shirye sama da 100 a fannin samar da makamashi mai tsabta da kiyaye muhalli a kasashen Afirka. Misali a kasar Habasha, tashar Adama da ta Aysha da kamfanonin kasar Sin suka gina, wadanda ke samar da wuta ta amfani da makamashin iska, sun bunkasa makamashi mai tsabta, wadanda suka samar da tabbaci ga bunkasuwar masana’antu da ma rayuwar al’umma a kasar.

  • Shugabar Tanzania Za Ta Zama Shugabar Afirka Ta Farko Da Za Ta Ziyarci Sin Bayan Babban Taron Wakilan JKS Karo Na 20

A kenya, tashar samar da wuta ta amfani da makamashin rana ta Garissa da kamfanin kasar Sin ya gina, ta kasance irinta mafi girma a gabashin Afirka, wadda tsohon shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyyata ya taba bayyana ta a matsayin wadda ta taimaka wa Kenya wajen dogara da kanta wurin samar da makamashi mai tsabta.
A cikin shekaru 10 da suka gabata, ra’ayin muhimmancin kare muhalli ya yi ta kara zame wa al’ummar Sinawa jini da tsoka.

A yayin da ake kiyaye saurin bunkasuwar tattalin arziki a kasar, yawan iskar Carbon da aka fitar a kasar ma ya ragu ainun, baya ga muhallin halittu da yake dada kyautata, kasar Sin ta samu gaggarumin ci gaba ta fannin kare muhalli.

A sa’i daya kuma, kasar Sin ta yi kokarin rungumar makomar dan Adam ta bai daya, inda ta yi iyakacin kokarinta wajen samar da fasahohinta ga kasashe masu tasowa ta fuskar kiyaye muhalli. Kawo yanzu dai, kasar Sin ta samar da kudi yuan biliyan 1.2 kwatankwacin dala miliyan 165 wajen aiwatar da hadin gwiwa da kasashe masu tasowa don tinkarar matsalar sauyin yanayi, baya ga kuma daddale yarjejeniyoyin hadin gwiwa 43 tare da kasashe masu tasowa 38, tare da horar da ma’aikatan kula da sauyin yanayi kimanin 2000 daga kasashe masu tasowa sama da 120.

LABARAI MASU NASABA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Jam’iyyar kwaminis mai mulki a kasar Sin a babban taron wakilanta na 20 da aka kammala kwanan nan ba da jimawa ba, ta tsara taswirar gina kasa mai tsarin gurguzu ta zamani, inda kuma ta jaddada cewa, “ya kamata kasar Sin ta zamani ta kasance yadda dan Adam ke zaman jituwa da muhalli”, tare da tsara ayyukan da za a sanya gaba a wannan fanni.

Ban da wannan, ta kuma yi nuni da cewa, ya kamata a rungumi makomar dan Adam ta bai daya, “a tsaya ga kiyaye muhalli, tare da sa kaimin gina kyakkyawar duniyar dan Adam mai tsabta.” Ta hakan muke iya hasashen cewa, nan da ba da jimawa ba, kasar Sin ba kawai za ta kasance mai karfi ta fannin tattalin arziki da al’adu ba, tabbas kuma za ta kasance mai kyakkyawan muhalli.

Tabbas kuma kasar za ta kara samar da gudummawarta wajen tabbatar da kyakkawar duniyar dan Adam da ma dauwamammen ci gabansu.(Mai zane:Mustapha Bulama)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal
Daga Birnin Sin

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025
Daga Birnin Sin

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
Next Post
Hana ‘Yan Nijeriya Bizar Dubai Manakisa Ce, In Ji Gamayyar Matasa

Hana ‘Yan Nijeriya Bizar Dubai Manakisa Ce, In Ji Gamayyar Matasa

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

October 10, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

October 10, 2025
Kasar Sin

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Matatar dangote

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

October 10, 2025
Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

October 10, 2025
Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

October 10, 2025
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.