• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Soke Zaben Fidda Gwanin PDP A Kaduna Ta Tsakiya, Ta Bada Mako 2 A Sake Wani Zaben

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Kotu Ta Soke Zaben Fidda Gwanin PDP A Kaduna Ta Tsakiya, Ta Bada Mako 2 A Sake Wani Zaben
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kaduna, ta soke zaben fidda gwanin da jam’iyyar PDP ta gudanar a mazabar Kaduna ta tsakiya sakamakon wasu kurakurai. 

Kotun ta umarci jam’iyyar PDP da ta sake gudanar da sabon zaben fidda gwani na dan takarar Sanata na jam’iyyar a cikin kwanaki 14.

  • An Mayar Da Tubabbun Mayakan Boko Haram 3,500 Unguwanninsu A Jihar Borno
  • Rashin Tsaro: Buhari Ya Kalubalanci ‘Yansanda A Kan Matsalar Tsaro 

Mai shari’a Muhammed Garba Umar na babbar kotun tarayya da ke Kaduna, wanda ya yanke hukunci a ranar Laraba a kan shari’ar ya ce “Duk korafe-korafen da mai shigar da karar ya yi na da yawa, haka ma hukuncin da INEC ta yanke na gudanar da sabon zaben fidda gwani da ba a yi ba daga baya, kamar yadda sakamakon ya gudana, ikirarin da wanda ake tuhuma ya yi watsi da shi.”

Mai shigar da karar, Usman Ibrahim, ta bakin lauyansa, Samuel Atung, (SAN), ya garzaya kotu yana kalubalantar fitowar Lawal Adamu a kan rashin kuri’ar da aka kada masa, inda ya roki kotun da ta rushe wannan zaben tare da bai wa duk wani mai bukata dama daidai gwargwado don gwada farin jininsa.

Atung ya bayar da hujjar cewa wanda yake karewa yana da faifan bidiyo da bayanan da suka nuna cewa wakilai sun kada kuri’a wadanda sakamakon shari’ar da ya yi nuni da su shi ne rushe sakamakon zaben fidda gwanin da kuma soke sakamakon zaben, inda ya kara da cewa majalisar zartaswar jam’iyyar PDP ta kasa ta nemi hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa.

Labarai Masu Nasaba

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

Hukumar INEC ta sake gudanar da sabon zaben fidda gwani kawai don wanda ya karewa ya tattaro mabiyansa zuwa wurin da aka yi zaben a banza.

Lauyan Usman Ibrahim, Samuel Atung, (SAN) da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan yanke hukuncin, ya tabbatar da cewa kotun ta zartar da hukunci ne bayan nazari da ta yi.

Atung ya ce, “Bayan da jam’iyyar PDP ta Kaduna ta tsakiya ta zabi dan takararta a zaben 2023, abokin takararmu ya rubuta koke ga kwamitin daukaka kara na jam’iyyar yana kalubalantar sakamakon zaben.

“Muna da hujjojin bidiyo kan hakan kuma kwamitin ya yi la’akari da rokon da muka gabatar kuma ya mika shawararsa ga kwamitin zaben wanda a cikin hikimarsa ya yi kira da a sake zaben fidda gwanin.

“Jam’iyyar PDP ta rubuta wa INEC wasika, ta sanar da ‘yansandan Nijeriya, jami’an tsaron farin kaya da sauran masu ruwa da tsaki game da matakin da ta dauka na sake gudanar da zaben fidda gwanin na shiyyar Sanata Kaduna ta tsakiya, wanda abin farin ciki ne.

“Abin takaici a ranar da aka saka, abokin aikinmu, bayan ya tattaro magoya bayansa zuwa wurin da za a sake zaben fidda gwanin, sai aka ce ba za a ci gaba da gudanar da zaben ba saboda yadda mahukuntan suka ba da umarni.

“Mun zo kotu ne muna neman adalci a wannan takin kuma alkali ya yanke hukuncin cewa jam’iyyar ta bi matakin da kwamitin kasa ya dauka sannan ta sake gudanar da sabon zaben fidda gwanin nan da makonni biyu.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KadunaKotuPDPSanataSoke ZabeZaben Fidda Gwani
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ziyarar Da Shugabar Tanzaniya Za Ta Kawo Sin Za Ta Bunkasa Alaka Tsakanin Kasashen Biyu Zuwa Wani Sabon Matsayi

Next Post

Sin Ta Sanar Da Shirin Bunkasa Fasahar VR

Related

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa
Manyan Labarai

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

4 hours ago
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…
Manyan Labarai

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

5 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

15 hours ago
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo

24 hours ago
Buhari Ba Mutum Ne Mai Son Abun Duniya Ba – Gowon
Manyan Labarai

Buhari Ba Mutum Ne Mai Son Abun Duniya Ba – Gowon

1 day ago
Tinubu Bai Taɓa Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Bai Taɓa Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista

1 day ago
Next Post
Sin Ta Sanar Da Shirin Bunkasa Fasahar VR

Sin Ta Sanar Da Shirin Bunkasa Fasahar VR

LABARAI MASU NASABA

Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

July 11, 2025
Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

July 11, 2025
NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

July 11, 2025
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

July 11, 2025
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.