Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, ya ce ya daina karanta labarai a shafukan sada zumunta.
Tinubu, wanda akai-akai yana sabunta ingantattun hanyoyin sadarwar sada zumunta da sunansa, ya bayyana hakan a cikin wani faifan bidiyo da aka yada.
- Yadda Za A Tsaftace Hammata Da Cinyoyi Su Yi Kyau
- Zamantakewar Aure Tsakanin Miji Da Mata: Wa Aka Fi Zalunta?
“Ba na duba kafafen sada zumunta; suna daga min hankali. Idan na karanta, nakan sa jinina ya hau sannan na fusata. Ba na karanta komai a can, don haka idan ina son jin wani abu; ‘Ya’yana ko ma’aikatana ke wannan, idam na gaji, sai na ce don Allah a manta da komai!”
Tinubu, wanda ke kan gaba a yakin neman zaben 2023, ya ce kafafen sada zumunta na daga masa hankali.
Yayin da yake karkare jawabinsa a gangamin yakin neman zabensa da aka gudanar a Jos a ranar Talata, ya sha fama da zamewar harshe yayin da ya yi kuskuren yi wa jam’iyyar PDP addu’a a lokacin da ya ke kokarin ambaton jam’iyyarsa.
Hakan dai ya jawo cece-ku-ce a shafukan sada zumunta yayin da masu suka suka yi wa dan takarar jam’iyya mai mulki suka ce bai cancanci zama shugaban kasa ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp