• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zulum Ya Nemi Afuwar Atiku Kan Harin Da Aka Kai Wa Tawagarsa A Borno

by Abubakar Abba
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Zulum Ya Nemi Afuwar Atiku Kan Harin Da Aka Kai Wa Tawagarsa A Borno
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya nemi yafiyar dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP Atiku Abubakar, kan harin da ake zargin wasu ‘yan bangar siyasa da ba a san ko su waye ba suka kai wa ayarin tawagarsa a jihar.

Wannan na zuwa ne daidai da ya sha alawashin cewa, a karkashin mulkinsa, ba zai bari duk wata jam’iyyar adawa a jihar ta ci zabe koda na mazaba daya ba a zaben 2023.

  • Matan Kiristocin Arewa Sun Yi Wa Atiku Alkawarin Ruwan Kuri’a
  • Sirikin Buhari Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Kaduna

Zulum, ya sanar da hakan a yayin da yake yi wa magoya bayan APC da masu ruwa da tsaki jawabi lokacin kaddamar da shugabanni da sakatarorin da kuma ‘ya’yan cibiyar yakin neman zabe a gidan gwamnatin jihar da ke a Maiduguri.

Ya ce, abin dariya ne ‘yan jihar da ke zaune a wasu garuruwa sama da shekaru hudu, suka fara yin tururuwa zuwa jihar a karkashin jam’iyyun adawa daban-daban, musaman PDP suka kuma fara neman goyon ‘yan jihar don zaben 2023.

A cewarsa, “Ina son na sanar da cewa, APC a karkashin mulkina, za ta tabbatar cewa, babu wata jam’iyyar adawa a jihar da za ta ci zabe a 2023”.

Labarai Masu Nasaba

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Ya kara da cewa, “abin takaici ne ganin wasu masu neman madafun iko a cikin mataciyyar PDP a jihar a yanzu suna shigowa Maiduguri da Naira 500,000 zuwa Naira 600,000, inda suke raba wa mutane don yin kamfen din bataci ga APC, bayan sun manta da cewa, Borno gidan APC ne.

Ya ce, “APC ba ta jin tsoron duk wata jam’iyyar adawa, musamman ganin cewa, APC a karkashin mulkinna a shekaru uku da suka wuce, mun yi kokari wajen samar da tsaro, ayyukan yi, tallafawa matasa da mata gina wa da kuma mayar da miliyoyin ‘yan gudun hijira zuwa matsagunan su na ainahin.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCAtikuBornoPDPZulum
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matan Kiristocin Arewa Sun Yi Wa Atiku Alkawarin Ruwan Kuri’a

Next Post

Gwamnatin Kebbi Ta Zargi Aliero Da Wasu Kan Yi Wa Jihar Zagon Kasa Kan Wasu Ayyuka

Related

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

2 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

14 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

19 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

23 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

2 days ago
An San Masu ÆŠaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu ÆŠaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

2 days ago
Next Post
Gwamnatin Kebbi Ta Zargi Aliero Da Wasu Kan Yi Wa Jihar Zagon Kasa Kan Wasu Ayyuka

Gwamnatin Kebbi Ta Zargi Aliero Da Wasu Kan Yi Wa Jihar Zagon Kasa Kan Wasu Ayyuka

LABARAI MASU NASABA

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.